Showing 1 words to 3000 words out of 23627 words

Chapter 1 - BA KOWANE SO BANE Hausa Novels by Ouummey.txt

22 Jan 2026

22

MAI DAKI...

4

NA

HAJ. HAFSAT C. SODANGI

(Mrs. Yunus Abdullahi Dabai)

1

GODIYA

Godiyata har kullum ga Allah take, Masanin yau

da gobe, mai kowa mai komai, Gwani mai hikima

wanda yayi halitta tasa duka bibiyu, ya kuma halicci

mutum da Aljan don su bautata mishi.

Tsira da Aminci su tabbata ga cikamakin

Annabawa shugaban Manzanni, Annabin Rarshe

Muhammad (SAW) da Alayensa da Sahabbansa da

wadanda suka bi ma tafarkinsa na gaskiya har zuwa

ranar Alkiyama, amin.

Godiya mai yawa gare ku makaranta litattafaina,

na kusa da na nesa, Ubangiji ya saka da alheri ya

kuma kara karfafa zumuncin da ke tsakani, na gode.

SADAUKARWA

Sadaukarwar littafin ta Iyayena ce, Alhaji Chindo

Muhammad Sodangi da Hajiya Fatima Musa

Sodangi, Ubangiji ya saka muku da alheri ya kuma

Rara muku lafiya amin.

2

TUKUICI

Tukuicin littafin naki ne:

KHADIJA CHINDO SODANGI (Mrs Nasiru Idris)

JINJINA

Jinjinar littafin taki ce Amarya ba kya laifi

(Maman Umar) Zuhuriyya Ibrahim (Mrs Lawal

Chindo Sodangi), Ubangiji ya raya Umar da imani.

FATAN ALHERI GARE KU

Fatima Abdulkadir Kazaure

Hafsat Iliyasu Unguwar Rimi

Khadija Usman Nasarawa

Nafisatu Ibrahim Muhammad

Fatima Ahmad Shehu Kaduna

Maryam Muhammad Gusau, Zamfara

Umaima Abubakar Umar

Maijidda Uba Magaji

Na gode, Ubangiji ya saka da alheri, amin.

KUNA RAINA

Hajiya Maryam (Mami) Dan Hassan

Hajiya Jamila Ibrahim Na Bature

Hajiya A'isha Balarabe (Jazan)

UbangiJ1 ya bar zumunci amin.

3

LITTATTAFAN SODANGI:

Uwar miji

Naga ta kaina

Rabon kwado...

Cikar alkawart

Wayyo duniya

Yi wa wani...

Abu naka...

Mata ma su duniya

Nufin Allah

Kifin na ganinka..

Daga Kin gaskiya...

Da kamar wuya...

Mai uwa..

Duk daya...

Mata da kicin dinsu

Wacece ni?

Wata fuskar...

Mijin ta ce

Garin banza...

Ga ni gare ka

Biyan bukatar rai

Shamaki

Hattara

Kyautata

4

Ayi dai mu gani..

Tabbataccen al'amari

In kunne ya ji..

Halin rayuwa

Mai daki...

Littattafan ba sa nufin yi da wani ko

habaici ga kowa, sai dai an rubuta su ne

don fadakarwa da nishadantarwa, ana

neman afuwa ga duk wanda yaga wani abu

yayi kamar abinda ya shafe shi, ba da shi

ake ba dace ne kawai.

5

MAI DAKI...4

Sai da Babana ya dawo ne magana taso ta

lalace, don kuwa cewa yayi ba zai karbi

kayan Ahmad ba.

Shiru nayi a daki cikin wani yanayi, yayi ta

fada dalilin da yasa Umma ta bari aka sauke.

Itama dai bata ce komai ba, Yaya Auwalu

ya kira yace ya nemo mota a mayar da kayan

ba ya so. Ganin haka ne yasa Baba Ladi

diddingisawa ta same shi ta ce wai wannan

fadan da kake yi na meyene?

Na jin haushin yayi wa Mahaifiyarshi

biyayya ya saki Maijidda iye? Ina

tambayarka?"

Ya ce, "Subhanallahi Haj..." ta ce, "Kada

ka ce min komai, idan ba haka ba to menene?

Na ce me yayi maka?

Ai bai yi maka komai ba in baya ga hakan.

Haba! Wane irin abu ne haka, ka sa a mayar

mishi da kaya kayi abin kunya ka tonawa

kanka asiri ya gane abinda yayi ya bata maka

rai kai ka sani." Wai! Shiru Babana yayi ya

koma daki, ni kuma na dan ji dadi don kuwa

har a yau bana jin haushin Ahmad. Gagarumin

6

biki muka yi, cikin wadata don kuwa abinci

kala-kala aka yi, fate, shinkafa fara da miya,

dafa duka, alala, tuwon semo da shinkafa da

miyoyi daban-daban.

Ga kuma masa, kowa yana cin abinda yaga

dama ne.

Ta bangarena kuwa kwalliya nayi bana

wasa ba, don kuwa dinkunan da Ahmad ya

aiko min da su na saka, sun kuma amshi jikina

tsaf.

A gidan da Yaya Auwalu ya karba haya aka

saka Amarya wanda yake daf da namu.

An kuma watse biki lafiya, kowa ya tafi in

banda Baba Ladi wacce take zaune saboda

asibitin da zata fara zuwa, saboda ciwon kafa

da ke damunta.

Hakan yayi mun dadi ba kadan ba, don

kuwa katifata na dauko na dawo da ita dakin

Baba Ladi.

Wani lokaci sai mu kai karfe sha biyun dare

muna hira tana bani labarin mijinta da ya rasu.

Mahaifin Babana da irin gwagwarmayar da

ta sha da kishiyoyinta da a yanzu suka zame

mata 'yan uwa.

7

A duk sanda ta bani labarin su sai na ce oh,

amma dube ku Baba Ladi kamar ba ayi irin

wannan zaman ba.

Sai tayi murmushi ta ce, eh to wanda ya

hada ma ai ya raba tunda ina yake?

Bana shekaru ashirin kenan dukkanmu

kuma muna nan, ko wace ce zata fara bin shi a

cikinmu? Sanin gaibu sai lillahi.

Na ce, amma fa ni sai nake gani kamar gara

mun matsalar kishiya a kan ta uwar miji.

Baba Ladi ta waiwayo tana murmushi ta

kalle ni ta ce, saboda matsalar uwar miji ce da

ke ko?

Amma in ban da haka ai matsala bata wuce

kishiya ba. Sai dai idan kawaiba ka da

fitinanniya.

Ba zan yi musu da Baba Ladi ba da na gaya

mata cewa ita kishiya duk fitinarta ai ba za ta

saka mijinka a gaba ta ba shi umarnin sakinka

ya kuma sake ka din ba, kenan dai da

bambanci.

Kwanci tashi babu wuya sai dai kawai idan

Allah bai kaddara maka ganin gobe ba.

8

An wayi gari ne a yau na gama Iddah ta. A

karo na Rarshe kuma da nayi nufin fuskantar

gaskiya game da maganata da Ahmad ta kare.

A daren jiya kuma na kwana ne ina tunanin

abin da ya kamata nayi shi ne, komawata

Makaranta wanda nasan da wuyar gaske

Babana ya bar ni.

Umma dai ina ta yi mata maganar cikin

dabara nake 6ullo mata da kuma muhimmancin

karatun 'ya mace da kawayena irin su Sadiya

Tanimu.

Wacce a yanzu take aiki a babban asibiti, ta

gama karatunta na aikin jinya.

Umma ta ce, eh hakan yana da kyau amma

ai kuma naga bai kai darajar aure ba.

To gaskiya Umma ta fada, don kuwa ko ba

komai ai gani da Abulkhairi da ke can tare da

Babanshi.

Yanzu shekarunshi hudu ne har da watanni.

Idan da na haihu a gidan Ahmad da yanzu

abinda na haifa yayi wayo.

Tuna abinda ya faru da ni da cikina a

lokacin yasa zuciyata tayi mun wani iri.

9

Amma har yanzu Sadiya tana nan bata y

auren ba tukunna.

Ganin yadda Ummata ki maganar

makarantata yasa jikina yayi sanyi da yawa.

Anya Babana zai yarda kuwa? A wancan

karon ma ga yadda muka yi da Babana to

ballantana kuma yanzu. To amma duk da haka

Makarantar ita ce mafita a gare ni, tunda dai

karatu ba ya hana aure.

Sai dai ta ya ya zan bullo mishi?

Muna zaune da Baba Ladi a tsakar gida

hantsi muke sha, yayinda nake shafe mata

kafarta da wani mai da aka bata a asibiti.

Muna kuma 'yar hirar mu mai dadi. Umma

ce a kicin, kokarin damawa Baba Ladi kunun

tsamiya take yi.

Saboda wai bakinta da baya mata dandano.

Wayata tayi kara, na dauka.

Ahmad ne sai dai jikina a sanyaye na dauka

na shiga daki don kada Umma taji ta gane da

shi nake magana.

Bata hana ni magana da shi ba sai da kuma

a yanzu da na gama Iddah menene alakata da

shi?

10

Wannan ita ce tambayar. Har ta gama

kararta ina rike da ita a hannuna ban dauka ba.

Ta sake fara wani sabon rurin kamar kada

na dauka amma kuma sai na kasa.

Sallama na fara yi mishi tare da gaishe shi,

sannan muka yi shiru kamar dai ba kudi ne ke

tafiya ba. Shirun ne yayi yawa na ce ya

kasuwa?

Ya ce, Lafiya Hauwa'u, na kira ki ne naji

lafiyarki." Na ce, To na gode.

Na ajiye wayar ina jin haushin abinda yasa

na dauka.

Shiryawa nayi da daddare na nufi gidan

Yaya Auwalu, don nayi mishi magana kan

Makarantata.

Don nasan idan ya nunawa Babanmu yana

da ra'ayi a kan karatuna babu mamaki nayi

nasara ya sassauto.

Matarshi na samu Samahatu tana ta hidimna

dashi tana kokarin hada mishi abincin dare.

Sha'awarsu ta kama ni.

Yaya Auwalu yayi sa'ar mata nitsattsiyar

yarinya, ga kunya da kirki. Cikin girmamawa

ta gaishe ni ta juya tana hado wani abincin.

11

Kasancewar kicin din ta falo yasa Yaya

Auwalu ya ce idan Hauwa'u za ki hadowa

abinci bar shi zamu ci a nan.

Ta ce, To don haka ta miko min cokali na

saka a plate din Yaya Auwalu muna ci tare.

Sai da muka gama cin abinci sannan na ce

Yaya wurinka nazo. Dukkan nutsuwarshi ya

tattaro ya zuba mun ido ya ce lafiya dai ko?

Na ce, Lafiya kalau, ya ceTo

Alhamdulillahi muje waje. Na ce, A'a zamu

iya yin magana a nan babu komai ai.

Duk da haka sai da Samahatu ta shiga daki

har da ce matan da nayi tayi zamanta kawai.

Na dan yi mishi 'yan bayanan da zan yi

mishi kan bukatata ta komawa Makaranta, da

kuma muhimmancin hakan a wurina idan an

bar ni.

Karshe nayi mishi bayani mai gamsarwa

kan hakan ba zai hana ni aure ba idan damar

hakan ya samu.

Ya dan yi shiru ya ce, "To ai matsalar a

wajen Baba ne da kyar zai yarda don ba ma zai

kalli abin ta wannan bangaren ba.

12

Kuma ni nasan yana da gaskiya don kuwa

karatu tuntuni ba a yishi ba sai yanzu ne za a

tsiri yi Hauwa'u zai yiwu?

Na ce zai yiwu Yaya, ai komai sa kai ne

1dan mutum yayi niyyar yi. Ya ce, To haka ne.

Muka fito da Yaya Auwalu yana rakoni

gida muna 'yar hirarmu.

Kwata-kwata ban kula na ganshi ba,

Abdussamad ne. sai da naji suna gaisawa

Yaya Auwalu.

Na daga kai na hango shi tsaye kofar

gidansu, hannayenshi zube cikin aljihun

wandonshi.

Duk da dare ne bai hana ni gane cikar da

yayi ba. Ban ce mishi komai ba gida kawai na

shige ina tuna rabona da ganin Abdussamad

tun kafin aurena da Alhaji Ahmad.

Kwanaki biyu ne bayan nan ya shigo

dakinmu ya same mu muna hira da Baba Ladi,

ya zauna.

Mun jima muna hirar dashi sai da ya fara

shirin tafiya ya ce, to ke idan aka ce an bar ki

ki koma makarantar daga ina za ki faro?

13

Cikin sauri na kalle shi na ce, Yaya Baban

ya bari ne? ya ce, eh ya yarda amma kin san ba

ki da takardar Secondary school ko?

Na ce, eh. Ai niyyata na koma daga inda da

ma na tsaya, wato SS 2. Ya dan yi shiru ya ce,

To amma me yasa ba za ki yi ertra moral

classes ba sai ayi miki register ki rubuta

(WAEC) da (NEC0).

Yayi min register gaba daya har da kuma

reciept na biyan extra moral classes.

Na tsaya bayanin murnar da nayi ma batawa

ne kawai. Haka nan shi kanshi Yaya Auwalu

yayi ne don naji dadi.

Tunda ba wani kudi ne da shi ba, dawainiya

tayi mishi yawa, a yanzu mafi akasarin hidimar

gidanmu a kanshi take, ga kuma na gidanshi.

Ban san dalili ba sai kawai naji tamfar an

yaye min dukkanin matsalata. Ban wani bata

lokaci ba a washegarin ranar ne kawai na fara

zuwa daukar karatuna don fara shirin zana

jarrabawar shaidar gama Secondary school.

Kwanaki kadan da fara zuwana karatu na

dawo da yamma ina shan furar da na samu

Baba Ladi ta ajiyc mun.

14

Sai kawai ga dan aika wai ana sallama da ni

a waje. Mamaki ya matukar kama ni.

A sanina dai ban taba kula wani ba tun

gama Iddah ta, na ce ma dan aiken waye ne?

Baba Ladi ta ce, mu ki ke tambaya ko shi da

aka aiko? Yarinya tayi aure ta zauna a dakinta

wani sanabe wai zata yi karatun da da can ba a

yi ba.

Nayi lullubi na fito na bar Baba Ladi tanata

sababinta.

Hango wata dalleliyar mota nayi sai kashe

ido take yi, sai dai tun. daga nesa mamaki ya

kama ni, Ishak ne.

Na kama baki ina mamaki tare da murmushi

a raina dai ina cewa to wane irin kudi wannan

mutumin ya samu haka?

Na karasa inda yake na ce, To ya ba ka

karaso ba ku gaisa da su Umma. Ya dan yi

murmushi ya ce, Hajiya Hauwa'u kenan ai sai

na samu fuska a wurinki tukunna kada nayi

karanbani.

Komawa nayi na sanar da Umma zuwan

Ishak, na jawo tabarma nayi mishi shimfida

tare da ajiye mishi ruwa.

15

Suka gaisa da Baba Ladi da Umma, sannan

ya koma motarshi ya zauna.

Nima can na sake binshi. Na tambaye shi

Yaya da yaran duka, Ya ce suna nan kalau.

Satin can ma ina Kaduna tare da su na ma

sanar da su cewa zan zo, Yaya ta ce na gaishe

ki sosai.

Na dan yi murmushi don kuwa raina yana

Son Yaya. Ya dan kalle ni ya ce, Jininku ya

hadu da na Yaya.

Na ce, To ya harkoki da iyali?

Ya ce, "To harkoki kam mun gode Allah,

amma iyali kam ai kema kin dai tambaya ne

kawai don jin baki?

Ban ja zancen ba a nan na bar shi don ba

doguwar magana nake nema ba.

Bai wani jima ba ya sa hannu a aljihun mota

ya dauko kudi masu auki ya miko min.

Na kalli kudin na kalle shi na dan girgiza

kai na ce a'a na gode.

Ya zuba min ido yana kallona ya ce ba za ki

kar6a ba saboda me?

Na ce, saboda ba ni da buRatar su. Take

yanayinshi ya canza alamar ranshi ya sosu, ya

16

Ce to amma ai ko ba ki da bukata da sai ki

karba don na gane ina da mutunci a wurinki.

Ba na ba ki ki ki karba ba, tunda nima ban

ce kina da bukatar su ba, kyauta ce nayi niyya.

Nasa hannu na karba tare da cewa, Na gode.

A tsakar gida na samu Umma da Baba Ladi

suna 'yar hirarsu da alama kuma kan zuwan da

Ishak yayi ne.

Baba Ladi ta ce, To ina tabbatar muku dai

wannan mutumi idan ko me yazo yake nema ta

tattara a kuma daura mata aure da shi ta koma

ta rike danta.

Tunda ma da alama a gidanshi nata arzikin

yake, ba gashi shi wannan da ta aura ba 'yan

rabuwarsu bata haihu ba.

Sannan shi mutumin da yayi saki ya dawo

yake neman a komai ai alama ne na zai gyara

kuskurenshi na baya.

Ina jinsu ban ce musu komai ba haka nan

ban ma nuna musu kudin ba, don kuwa nasan

halin Umma.

Da daddare bayan mun idar da sallar Isha'i,

hira muke yi da Baba Ladi ta kara sako mun

zancen Ishak da zuwan da yayi.

17

Na ce, kai Baba Ladi kenan, kuma kawai

daga mutum yazo ba ki san abinda ya kawo shi

ba sai ki ce a bishi a sasanta.

Saboda zamana ya ishe ki ba kya son ganina

ko ya ya? Ta ce, a'a ba fa haka nake nufi ba,

zato nake ko maganar komawarki ce ta kawo

shi?

Na ce, To ba haka ba ne, ranar da yazo a

kan maganar ko-men zan kawo shi wurinki.

Ni kaina nasan zamana a gida baya yiwa

mahaifana dadi, to amma lalura idan ta samuu

mutum hakuri yake yi da ita, ya jira lokacin da

Ubangiji zai warware mishi ita.

Wannan yana daga cikin dalilin da yasa na

dukufa wajen ganin na dage na samu nasara a

kan karatuna.

Kyakkyawan shiga nake yi ta mutunci a duk

lokacin da zan tafi Makaranta.

Dogon hijabi nake sakawa, haka nan ko a

Makaranta bana shiga harkar kowa.

Karatuna kuma nake yi bil hakki da

gaskiya. Yau ma fitowa nayi zan tafi

Makaranta cikin kyakkyawan shiga.

18

Har na hauro saman layinmu, daga kan da

zan yi sai muka hada ido da Abdussamad da ke

tsaye kofar shagon askin unguwar.

Shima ni yake kallo, ban tsaya ko tunanin

gaishe shi ba wucewa ta kawai nayi. Sai dai a

raina tunani nake yi abinda ya dawo da shi

cikin ranakun aiki.

Tunda a sanin da nayi yana zaune ne a

Abuja inda yake aiki a Ma'aikatar Sufuri.

Tun a wancan karon da yaro yayi mun

rashin mutunci ya fita mun a ka, don haka a

yanzu ma babu ruwana da sh1.

Sati guda cif da zuwan Ishak, sai kawai

gashi ya dawo abinda a take ya fassara min

abinda yake nufi.

Ko da dai bai budi baki ya furta ba. Nima

kuma ban ce mishi komai ba, baya ga fitan da

nayi ya gama maganganunshi ya sauke min

kayan masarufi iri-iri.

Na shiga gida bayan tafiyar shi. Tun daga

shigana jikina yayi sanyi saboda yanayin

kallon da Umma take yi mun.

Daga nesa kadan na nemi wuri na zauna,

amma na kasa sukuni.

19



Bata ce min komai ba, aikace-aikacenta take

tayi. Bayan ta gama ta shiga daki ne naji ta kira

ni.

Har a lokacin fuskarta bata washe ba. Ta

zuba min ido a durkushen da nake ta ce "Za ki

koma gidan shi ne?

Tambayar tayi mun wani iri, cikin sauri na

dago kaina na kalli Umma da itama ni take

kallo.

Idan za ki koma gidan shi ne ki fada saboda

na sanar da Babanku tun kafin ki karasa zubar

ma mutane da mutunci.

Cikin sauri na ce, "Umma kiyi hakuri ba

izinina yake nema yake zuwa ba, ganinshi

kawai nake yi.

Ganin shi kawai ki ke yi shi mahaukaci ne?

kina nufin idan da bai ga fuska a wurinki ba za

ki ganshi?

Tunda ki ke abubuwan da ki ke yi a gidan

nan ban taba ce miki komai ba, amma ki kwan

da sanin cewa a wannan karon kada ki sake

fitowa ki dawo gidannan ki zauna.

Hakan yana nufin sabon aure ne ko kuwa

ko-me don abin ya ishe ni haka, sannan na baki

20

kwanaki kadan mutumin nan ya daina zuwa

gidan nan ko kuma na shaidawa Babanku don

ya sani."

Dawowa daki nayi na zauna ina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login