Showing 3001 words to 6000 words out of 31076 words

Chapter 2 - HAUWA KULU Yar Cikin Badala Part 3 BY TAKORI.pdf

mai ko garwashi, tunda ba ni da ido, komai ma bazan iya ba Inna na taimakon ki,
na zama banida amfani?".
Zuciyar Inna ta karye, wani irin karyewa, cike da 'maternal love' wanda ya motsa mata, ta ce,
"Idan Allah ya nufa, da albarkacin tsarkin Al’qur’ani, da tsarkin mulkin Allah sai ganinki ya
dawo kamar na kowa tun a duniya HAUWA-KULU, sai kin ga idon ‘ya’yan ki, sai kun hada ido a
lokacin da kike shayar dasu, ina ji a jikina ba za ki dauwama cikin wannan halin na lalurar
makanta har abada ba. ubangiji yayi alkawarin kowacce cuta tana da magani, amma waraka
lokaci ce. Ina ji a jiki na takaitacciyar jarrabawar ki ce Hauwa mai zuwa ta wuce, da yardar Allah
sai kinga fuskar 'ya'yanki a lokacin da kike shayar dasu.

Kada ki kara cewa kin zama bakida amfani, duk mai nakasa indai ba zuciyarsa ce ta mutu ba
kuma ya tsaya ga neman ilmi ga kowa ina tabbatar miki zai iya komai da mai lafiya ke yi.
Allah da kansa ya ce, "Ad'uni Astajib lakum! Wato (Ku roke ni, Zan amsa muku)".
Ta daga hannu biyu sama tana fadin "Ya Allah Ubangijin sammai da kassai, ina Mai tawassuli
da sunayenka tsarkaka guda 99, a yau ni Safiya uwar Hauwa ina rokonka; Ka budewa
HAUWA-KULU idanunta ko kadan ne tun a gidan duniya darajar kaunar da ta ke yi wa
iyayenta”. Hauwa Kulu cikin tsananin hawaye da jin dadi ta ce, "Amin-Amin ya Allah Innata".
"Yanzu gaya min me ki ke so ki dafa masa sai mu yi tare?” Inji Inna.
Ta kara da cewa “duk uban aikin da kikeyi a Tashar kuka da kanoline kin manta, ai ke dinnan
ba sakaltacciyar mai lalura bace". Hauwa ta ce cikin jin karsashi ya dawo mata,
"Inna funkason fulawa da miyar taushe nake so in yi masa, ko kuwa alkubus da miyar ganye.
Na tabbata ya jima bai ci su ba, in kuma ya ci din, to ba irin na gidannan ba".
Inna ta yi murmushi tace, "an yi an gama Kuluwar Babanta. To mu yi duka biyun mana? Malam
dan gatan Kulu ya ci kala biyun. Bari in tattaro miki kayan hadin sai ki kwaba alkubus din da
funkason da hannunki, nikuma in dafa alkubus din, in kuma soya funkason".
Hauwa ta yi murmushin jin dadi, Inna ta gama ganeta fiyeda kowa a duniya, bataso nakasar
nan tata ko kadan ta maida ita useless (mara amfani), suka soma aikinsu tare suna yi suna hira
kamar kawaye.
A haka Malam ya tadda su a kitchen din wajejen karfe takwas na safe.
"Hauwa da Innarta girki ake yi mana haka?"
Hauwa na kwabin funkaso ta yi dariya ta ce, "Ni nake maka girki na musamman Baba, na sannu
da zuwa na tabbata zaka ji dadinsa".
Ya ce,"Allah yayi miki albarka. To ku gama in ba ki tsarabobinki daga Ubangidana, har da
na'ura mai kwakwalwa sabuwa dal a kwalinta ya aiko miki".
Hauwa ta ce. "Ai kuwa an koya mana amfani da ita kadan a makaranta, lokacin da muna aji
biyar, an gaya mana zamu iya amfani da ita muma ta duk hanyar da mutane ke amfani da ta a
matsayin 'assistive technology' ga masu lalurar idanu".
Can kuma ta dubeshi ta ce, "Baba baka gaya mana ina ka je ba, da abin da ya faru cikin
batan naka, rana daya muka rasaka, haka rana daya katsahan muka ganka cikin koshin lafiya
ka dawo. Ba tareda tsumi da dabarar mu ba.
​ Ni dai na san addu’ata ce Allah bai wofintar da ita ba, don bana yin sallah na tashi daga
inda nayi ta ban roki Allah ya bayyana min kai ba, ni nasan addua ta bata fadi ba, lokacin
amsarta ne Allah ya jinkirta min".
Malam Bilyaminu ya ce, “Tabbas Hauwa’u, addu’a ba ta taba faduwa kasa banza, don nima
na san tasirinta da alfanunta ne yau ya dawo da ni cikin iyalina lafiya da nisan kwana….".
“Assalamu alaikum. Inna me kike dafawa ne haka duk lokon nan ya dauki kamshi?”
Sai jin sallamar Dr. Sarham da korafinsa suka yi a gidan da safiyar Allah, wand aba lokacin
zuwansa bane yafi zuwa da daddare, misalin karfe tara na safe yau yayiwa gidan tsinke.
Kallo daya za ka yi wa Dr. Sarham ka san ya fito daga gida ne ba tare da shiri ba, don Malam
Isah ne ya kira shi da sassafe ya tabbatar masa Baban Hauwa ya dawo, har sun gaisa dashi
yau a masallaci wajen sallar asubahi.
Dr. sarham ya zo gidan ba shiri ba don ya yard aba sai don tabbatar da labarin Malam Isah.

Duk da dai ya san da kyar in zai fadi abinda bai gani ba. Ilai kuwa da Baban Hauwa ya soma
tozali tsaye a kofar kicin, suna hira shi da iyalinsa. Sarham ya lumshe ido yana murmushi
lokacin da ya karaso yayi musabiha da Malam Bilyaminu, yana kallon fuskokin wadannan family
da suka cika da annashuwa yau. "What a family!" Sarham ya gaya wa zuciyar sa cikin jin dadin
walwalar da suke ciki.
Inna ta amsa masa fuska fal annuri. Malam ya yi masa barka da zuwa tare da cewa su
karasa falo, suna shiga yana cewa, "ko ba a yi min gabatarwa ba, jikina da zuciyata sun gama
bani likita Sarhamu ne wannan".
Sarham yayi kasa da kai cikin girmamawa, ya ji wani irin farin cikin ganinsu haka complete
family kamar nasa iyalin, bakinsa da murmushinsa ‘from ear to ear’, wato daga jiyan zuwa yau
kadai har Malam Bilyaminu ya san da zamansa, wanda ke nufin yana da matsayi mai girma a
wajen Inna, (don ba zai ce a wajen Hauwa ba), ya san bazata iya bawa Babanta labarin sa ba
don ba damuwa tayi da shi ba sai ko Inna. Amma tabbas ya san ta bashi labarin saurayinta dan
polo.
Inna ta saka mishi funkason da alkubus din a nashi farantin ta zuba miya a karamin kwanon
Samira ta aje masa gabansa, bai yi fulako ba don kuwa bai karya kumallo ba ya fito, kai ko
wanka bai iya tsayawa yayi ba saboda wannan albishir din da Malam Isa yayi masa, Inna da
Hauwa suka kammala aikin su suka dawo falon suka karya kumallon tare. Sai da suka kammala
tsaf, kowa ya wanke hannu ya sha ruwa, suka sa Malam Bilyaminu agaba kamar sa hadiye shi,
har Sarham din ya kagu yaji inda ya shiga, malam Bilyaminu ya fara basu labarin abin da ya
fidda shi ranar daga gida, da rayuwarsa ta tsayin shekaru bakwai da yayi a ‘Kumasi’ ta kasar
GHANA.
"Asali muna da gona ta gado ni da dan uwana Zakari, wadda takardunta suke hannunsa,
kullum na yi niyyar karbar hakkina sai in ji kamar an mantar da ni. Rannan dai da karfin addu’a
Allah ya ba ni sa'a na taka same shi har wajen sana'arsa ta wankin hula, da zancen ya kamata
mu sayar da gonar nan tamu haka, mu ja jari mai tsoka, mu kama manyan shaguna ya fiye
masa sana'ar wankin hula.
Ni ma in samu in zama babban dealer na gwanjo, in dinga zuwa sarowa da kaina, maimakon
da da sai dai in sara hannun ubangidana. Wato ya zama cewa na samu jarin da zan dinga fita
kasashen ketare kawo gwanjo da kaina.
Zakari ya gama saurare na tas, sai cewa ya yi, shi babu wata gona a hannunsa, bai kuma
san da zancenta ba”. Na ce, to idan ya hana ni, wannan karon zan kauda ‘yan uwantaka, zan
sa hukuma ta kwatar min hakkina, zuwa shari’a a kan gado ba yau muka fara ni da shi ba. sai
dai wannan karon kotu zani ba gun mai unguwa ba. Amma ko sati biyu ba muyi da yin wannan takaddamar ba rannan ba kya gidaina shirin fita
kasuwa sai ga Zakari ya zo har zaurena ya same ni, tunda na yi tozali da shi gabana ya fadi,
mummunar faduwa, mukayi tozali da juna sai kaina ya soma sarawa, duniya ta soma juyamin,
sai ya miko min hannu ya ce, in ba shi takardun gidana da na saya a hannunsa, wallahi kamar
sihiri, babu musu babu jayayya ko bakinsa bai gama rufewa ba na shiga gida na fiddo su na
kawo masa.
Sai da ya karba ya saka a aljihunsa, sannan ya ce min cikin daga sauti na bada umarni.
"Tashi ka shiga duniya, kada ka tsaya cikin kasar nan, ka tafi ko can tsakiyar kasashen Africa
ta yamma ka rayu a can, ko bangon duniya kai duk inda mai ya kare maka".

Malam Bilyaminu yace, "Iya abin da zan iya tunawa kenan, sai ganina na yi a mota mai zuwa
kasar Ghana, kuma da yake ba ka raba dan kasuwa da kudi a jikinsa, sai ban rasa kudin biyan
kudin mota ba. Musamman da yake a jiyan ranar, na bude dealer din gwanjo na sayar.
Saukata a Kumasi ke da wuya kuma wallahi cikin hankalina nake komai, muna tunanin inda
za mu raba mu dan huta zuwa wayewar gari mu san inda zamu nufa na ji daga bayana an kira
sunana cikin matukar mamaki.
Ina juyawa na ga Alhaji Munkaila, wato Ubangidana wanda a wurinsa nake sarar gwanjo a
Kano, cike da mamaki yace me ya kawo ni kasar su? Anya lafiya kalau nake? Wa na sani a
Ghana me na zo yi kuma? Na samu bakina kai tsaye da cewa, "Neman na kai na fito!".
Alhaji Munkaila ya ce, “amma a sanina, daidai gwargwado Bilyaminu ai sana'arka na garawa
a Kano, na ga in ka kwance dealer ba ka kwana uku ta kare ka zo neman sabuwa ba.
Na ce masa ra’ayina ne barin Kano in dawo Ghana don in yi sana'ata a nan, ya fimin
kwanciyar hankali.
Alhaji Munkaila ya ce, Ina da wajen sauka ne? Na ce "ni fa Alhaji na dai zo Ghana ne. Amma
ban san kowa a cikinta ba, ban kuma san meyasa na zabeta ba”. Alhaji Munkaila yace min tun
a lokacin, ya fahimci ba cikin hayyacina nake ba shiyasa ma bai yarda ya barni na shiga gari
neman masauki ba yaji tsoron kada in fada hannun bata gari. Sai ya ce, tunda na ce nema na fito, to in bishi ya bani masauki mu ci gaba da sana'armu a
nan Kumasi yadda muka saba a Kano, don can din ma Ghana Gwanjo na garawa kuma ya bar
Kano ya dawo gida.
Ya gaya min yanzu ya dawo Ghana gaba daya saboda mahaifin sa ya kwanta dama, zai kula
da mahaifiyarsa da kannensa, dama kasuwanci kadai ke kaishi Kano, amma shi dan nan
Kumasi ne.
To kun ji yadda aka yi na samu Ubangida cikon taimakon Ubangiji ba tareda na tagayyara bat
un daga ranar dana sauka a Ghana, muka ci gaba da sana'armu ta shigo da gwanjo.
Alhaji Munkaila na da karfi sosai a sana'ar mu ta Gwanjo don kai tsaye yake zuwa kasar Italy
ya saro Gwanjo. Daga baya ma da ya koya mana ni da babban dansa Salisu yake turawa mu
saro, shi kuma ya rarraba.
Ba jimawa na iya manyan yaren Ghana tun daga yaren Akan, Ewe, Ga, har zuwa Dagbani
da Turanci tsilli-tsilli na 'yan koyo a bakin Salisu da abokan cinikayyarmu.
Lokaci-lokaci da yaga kamar na dawo hayyaci na na koma cikin nutsuwata Alhaji Munkaila na
yawan cewa ya kamata in je gida in ga iyalina haka, ko ya ce in daukoku, Sai in ce masa ba
yanzu ba, har ya gaji ya rabu da ni.
Mun samu alkhairi mai yawa a wannan sana'a tamu ta shigo da Gwanjo, har wani lokacin da
zamana haka ya dame shi ya yi min tayin auren kanwarsa Yahanasu wadda mijinta ya rasu ya
barta. Ni kuma na gaya masa cewa, har abada ba zan iya aure a Ghana ba, don na san
uwargidana ko mutuwa na yi ba za ta iya auren wani ba ni ba. Ya ce, to lallai in koma gida in zo
da ku.
A wannan karon na gaya masa hakikanin gaskiyar dake zuciyata cewa ko sunan garin Kano
bana son ji!
Alhaji Munkaila yace min shi da kansa ya fahimci al'amari na akwai saka hannu a ciki, da
shekaru suka yi gaba banida niyyyar komawa gida shi da kansa yasa wani shaihun malaminsa
ya dinga yi min addua a boye, ba tare da na sani bama. Idan ma wani makaru ne a jikina ya

roke shi ya kwance in koma ga iyalina ko in dauko su inda nake, in Kano ce bana so
kwata-kwata. Don a lokacin har gidan kaina da motar hawa na mallaka a kasar Ghana.
Rana daya na samu duk dabaibayin da ke zuciyata yana yayewa. Na ji hankalina bakidaya
ya dawo Kano.
Na zama ba abin da nake so irin in bude ido in gan ni cikin iyalina. Ga mafarke-mafarke da
nake tayi a kan Hauwa'u, wai ba ta da lafiya. Wani mummunan abu ya faru da ita. Rana daya ni
da kaina na samu Alhaji Munkaila na gayamasa ina da mata da 'ya dana baro, ina so in je in
taho da su Ghana, don ba zan iya kara zaman Kano ba, na fi jin dadin sabuwar rayuwa ta a
Ghana, wani bare sau dubu ya fiye maka dan uwa na jini.
Alhaji Munkaila kusan ya fi ni farin ciki da dawowar hayyaci na, don da kanshi ya saya min tikitin
jirgin zuwa Kano daga Ghana. Ya kawo tsarabobin sittiru na gwanjo masu karshen tsada na
turawa da na na'ura mai kwakwalwa ya ce a kawo wa Hauwa'u, kuma yana yi wa dansa Salisu
dana baro yana karatu a Italy kamun auren ta, don ya san zuwa yanzu ta girma. Na iso Kano lafiya, na hawo drop din taxi daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano na zo
har kofar gidana.
Na sha mamaki ganin sabon gida a muhallin gidana, sai da na tambayi mutane kusan uku ko
a nan kofar gidan ko inda Innar Hauwa da 'yarta Hauwa suke zaune ne? Ana ta tabbatar min
“eh a nan suke”, wani ya ce min amma ba su jima da dawowa ba, sannan na iya na shigo".
**** **** ****
Anan Malam Bilyaminu ya nisa, ya ce, "To kun ji wannan shi ne labarina. Da abunda ya faru
dani bayan barina gida. Zakari shi ya yi min makarun da ya kore ni don ya cinye gonar
gadonmu shi kadai. Na zo kuma na ji abin da ya yi wa gidana, don haka wannan karon nisa da
Zakari shi ya fi min alheri, ba zan iya shari’ah da shi akan abun duniya ba amma bazan kara
zama gari daya da shi ba, kuma ba zan yi shari'a da shi ba a matsayinsa na dan uwana na jini.
Na bar wa Allah ya saka mini, domin hakika ba ya yafe hakkin wanda aka zalinta.
Don haka ku yi shiri Hauwa da Innarta za mu tattara mu koma Ghana ne, ina nufin zamu bar
BADALA nan da kwana uku, son son samu ma gobe insha Allahu. Amma don in baku dama
kuyi sallama da abokan arziki irin likita, zamu tafi kwanaki uku masu zuwa in sha Allahu.
Ya juya ga Sarham ya ce, "Likita Sarhamu, Da nagari, dan albarka na ji duk halaccinka a kan
iyalina, ba ni da bakin gode maka ina rokon Ubangiji Ya fi ni godewa.
Allah ya yi maka albarka duniya da lahira, ya tallafi haularka a bayan idonka kuma Ya jikan
iyayenka, Ya kara yalwata musu kamar yadda ka zama yalwa kuma farin ciki ga iyalina.
Ina so kafin mu koma Ghana ka raka ni gun mahaifinka in yi masa godiya, don ni ban taba jin
mutum mai kyakkyawar zuciya karimi kamarka ba, wanda ba komai ba ne kyawun tarbiyyar da
ka samu daga garesu ne na taimakon mara gata da wanda yake cikin yanayi na bukatar tallafi
da lalura irin wannan…… Kafin kowa ya yi magana, aka ji Hauwa ta saka gunjin kuka har da sheshsheka, hankalinsu
ya koma gareta, Inna ta san Hauwa bata kuka na banza haka kawai mara dalili sai mai dalili,
shiyasa ta san tabbas kukan nan baka da zuci take yin sa, tana fadin, “ni ba zan koma Ghana
ba, ba zan iya barin Kano ba, b azan ma iya barin ko gidannan ba, ni Baba bazan iya barin
BADALAr da aka haifeni a ciki sabida zaluncin Baba Zakari ba”.
Ta kare zancenta da cewa "ba inda zamu je, muna da gida na tarihi, ina son zaman cikin
Badala, Baba da Inna ku barni in yi karatun da zan zama lawyer wallahi sai nayi muku

maganinsa".

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login