Showing 3001 words to 6000 words out of 23627 words

Chapter 2 - MAI DAKI (4) Book Complete By Hafsat C Sodangi.docx

22 Jan 2026

24

sakar zuci.

Ni kaina.nasan komawata gidan Ishak ba mai

yiwuwa ba ne, 1dan ba dole ya zama mun ba.

Haka an a yanzu da na samu aka lallaba

Babana ya hakura ya bar ni na komna

Makaranta wani abu yazo yayi sanadin da

damar ta subuce min ba zan so ba.

Hakan kuwa yana nufin da Babana ya ji

labarin zuwan Ishak, to zai dauki mataki, ne

kawai a kai.

Ilai ko ba a cika sati guda ba wannan karon

sai gashi ya dawo, abinda ya tabbatar mun da

maganar Umma da tace fuskata ya gani.

Na shiga dakin Umma tana kara gyaran

gadonta na ce, "Umma Ishak ne yazo.

Ta ce, To menene kuma nawa a ciki? Na ce,

eh dama na zo ne na gaya miki."

Ba ta ce mun komai ba, na juyo na kamo

hanyar fita waje. Yana hango ni ya saki

mumushi.

21

Al'amarin Ishak har mamaki yake bani,

idan na tuna irin zaman da muka yi da shia

matsayin mata da miji.

Uhum, wasu mazan ma dai sai a bar su,

basa taba sanin darajar matarsu a lokacin da

take zaune a gidansu har suyi tunanin ya

kamata su mutuntata don ta ji dadi.

Har sai ta subuce musu kuma sai su zo suna

ta faman kame-kame. Muna gama gaisawa na

ce mishi amma dai ya kamata ka san wannan

zuwan da ka ke yi ba shi da ka'ida.

Don kuwa idan har Babana ya ji labari ka

san ba zai ji dadi ba."

Ya dan yi murmushi har sautin murmushin

nashi ya bayyana, ya ce, "Eh ai babu wata

matsala, don kuwa Kawu ne zai zo jibi a kan

maganar saboda a yi komai nan ba da dadewa

ba.

Ba karamin bugun zuciyata maganar Ishak

tayi ba. Na dago kaina cikin mamaki da niyyar

nayi mishi magana.

Sai kawai yaci gaba.

22

"Kada ki samu damuwar komai, don kuwa

na dauka wannan auren da ki ka yi wata gada

ce ta halal ta mun ke don ki sake zama matata.

Ina so ki san har a yanzu ina sonki, na

rantse miki kuma na kasa yin wani auren ne

saboda kullum addu'ata bata wuce na ki dawo

gidana mu ci gaba da zamanmu ba cikin jin

dadi da kwanciyar hankali.

Kuma kema nasan kina sona, natsala ce dai

muka samu tare kuma da kaddara da

tsautsayi."

Takaicin Ishak ya kama ni, naji kamar na

shake shi na gana mishi azaba ko na samu na

huce,

Tun da ya fara magana shi nake kallo har

yayi shiru sannan nace ba addu'arka ce ta

karbu aurena da Ahmad ya mutu ba.

Don kuwa ba sakina yayi bisa son rai da

wulakanci ba, irin yadda kayi mun.

Sannan ban taba sanin cewa tunaninka zai

baka ni din zan kashe aure don na dawo

gidanka ba.

23

Ina so ka san babu tsautsayin da zai sani yin

hakan a yanzu. Nayi wani auren naji yadda ake

ji.

Na shaki iskar 'yanci da mutunci. Mijina ya

kula dani ya bani lokacinsa bai taba fita ya bar

ni ya dawo mun da tsakiyar dare ba.

Wani abu bai taba hada ni da shi ya zage ni

ya zagi talaucin iyayena ba. Ban taba yi mishi

wani kuskure ya wulakantani ya gana min

azabar duka irin yadda ka rinka yi mun a

gidanka ba.

Amma kai fa duk wadannan abubuwan a

gidanka suka same ni. Kana ganin kenan zan

sake dawowa gidanka da har ka ke karambanin

turo magabatanka gidanmu?

Jikinshi a sanyaye ya ce, "Haba Hauwa'u,

ina ce duk wadannan abubuwan sun faru ne

bisa kuskure kuma sun riga sun wuce.

Na ce, "Eh na sani sun riga sun wuce, amma

wucewar ba yana nufin zan sake tsoma kaina

cikin fitina ba ne.

Kayi hakuri amma ni har na fara shirye

shiryen komawa Makaranta."

24

Ya ce, "To amma Hauwa'u ai nayi miki

alkawura da yawa a baya da nake burin ganin

na cika miki su a ciki har da komawarki

Makaranta.

Na kuma yarda da kura-kuraina, na kuma

yarda zan gyara.

Na ce, Eh babu damuwa idan ka gyara nan

gaba, amma ni kam kayi hakuri.

Kaje kayi aurenka don kaima ka saukakewa

kanka damuwa."

Ishak bai yarda da abinda na gaya mishi ba,

don kuwa sai da ya turo magabatanshi.

Ba karamin godiya nayi wa Allah ba da ya

taimake ni na yiwa Umma bayanin komai a

ranar da Ishak din yazo.

Babana kuma ya gaya mishi shi a yanzu ba

zai tursasa mun auren kowa ba.

Idan mun sasanta a tsakaninmu to shi kenan

shi ba shi da matsala duk wanda aka yi.

Ban kara tsayawa sauraron Ishak ba idan

yazo, yazo har ya gaji. Kullum kuma yazo ya

aiko a kira ni hakuri nake ba shi na ce mishi ba

zan samu fita ba.

25

To ya dan kwana biyu yanzu bai zo ba.

Wani lokaci sai na ce ina ma da Ahmad ne ya

dawo?

Zan iya hakura na juya mishi baya haka

kuwa duk da matsalar mahaifiyarshi da

ya' yanshi? Zuciyata har yanzu shi take so.

Dan saukin abin ma shi ne, na hakura abin

kuma ya rage damuna.

Na kara fuskantar al'amuran karatuna

gadan-gadan har muka fara zana jarrabawa ban

fuskanci wani tsanani mai yawa ba.

Sakamako ya fito nayi nasara sosai, don a

yawan shekarun da nayi bana karatu ban yi

zaton zan samu result mai kyau haka ba.

WAEC na samu credit biyar, sai NECO na

samu shidda kuma a darussa masu

muhimmanci.

Kasancewar na ubuta har da JAMB sai

abin yazo mun kusan lokaci daya, don kuwa

JAMB din ma babu laifi an bani (Education

English).

Ranar murna a wajen Babana ba a cewa

komai, to ballantana kuma Yaya Auwalu.

26

Yana fama da asibitin matarshi saboda

laulayin da take yi, amma ba ya gajiya da tawa

dawainiyar.

Kullum kuma muka dan zauna zai gaya

mun ban da yawan yin kawaye saboda yadda

ake maganar 'yanmatan Jami'a.

Watanni uku ne kawai bayan nan sai gashi

har mun yi registration mun fara halattar aj

don daukar darasi.

Da iyakacin karfina na dage nake karatuna

saboda a yanzu shi ne abinda na tasa a gaba

don ganin bukatata ta biya.

A cikin sati guda da fara zuwana kuwa

tsakanina da kowa a ajin to gaisuwa ce ta

mutunci.

Ban ma ba da fuska ba saboda irin suturun

da nake amfani da su na mutunci wanda yasa

ake zaton ina da aure.

Na yarda da gargadin da Yaya Auwalu yayi

min, don kuwa a yan kwanakin fara zuwa

Makaranta da nayi naga yadda wasu 'yanmatan

suke ballagazar da kawunansu.

Wai su ga hadaddu wayayyu, kaga budurwa

takai ta kawo amma tana yawo da 'yar

27

fingilalliyar riga da matsattsen siket har ana

ganin shatan pant dinta.

Sannan babu gyale na mutunci ko hijabi,

kuma wai yar Musulma abin abin bakin ciki.

Yaya Auwalu dogayen hijabaí ya dunka

mun masu kyau har guda shida kala daban-

daban, ya ce gudunmawarshi kenan.

Ganin irin abinda ake yi na holewa ga

wadansu ni kuwa ban yi wannan wayewar ba

kuma bana fata sai akwai nake wucewa library

idan an yi break ko kuma na shiga cafë idan ina

da assignment din da zan yi.

A gida kuwa har Umma sai ta kara tattalina.

A duk sanda na dawo zan zo na samu abincina

kammale cikin food flask da dan abin sha.

Haka ma Baba Ladi duk da sanin da tayi

ana ajiye mun abinci itama duk abinda taci sai

ta ajiye mun nawa.

A yanzu bani da matsalar komai tafiyar da

al'amurana kuma nake yi cikin jin dadi, duk

wani nauyi ya sauka a Zuciyata.

Ban taba tuna Abulkhairi naji fargaba ko

rashin dadi ba don nasan yana hannu mai kyau.

28

Yaya mutuniyar kirki ce da ta san girma da

mutuncin kowa, da ace haka kaninta yake, to

da al'amarinshi yayi dadi.

Ina zaune na tasa abincin da aka aiko mun

daga gidan Yaya Auwalu a gaba zan fara ci.

Itama Samahatu kullum sai ta zubo min

abinci na daban duk da na gida da take aikowa

a babban food flask wanda wani lokaci ko

abincin dare ba ma yi saboda yawanshi.

Sannan ga laulayin ciki da ya tasata a gaba,

hakan ne yasa idan na dawo na samu nata shi

nake ci.

Idan kuma naci shi to shi kenan na koshi

saboda ni dama ba mai cin abinci ba ce.

Baba Ladi ta leka gefen gadonta ta jawo

kwano lafiyayyen kwadon zogale ne a ciki, ta

miko mun.

Na dan yi murmushi saboda nasan duk tana

yi ne don ta birge ni, ta nuna mun tana sona.

Hakan kuma kan sa naji dadi a raina.

Na ce, Baba Ladi Babanmu yana kawo miki

zogale ne saboda matsalarki.

Likita ne ya ce ki rinka cin zogale sosai

saboda yana magani, amma idan aka kawo

29

miki maimakon ki zauna ki ci ya ishe ki sai ki

raba biyu ki ajiye mun rabi, ni din da lafiyata

kalau.

Ta ce, eh nasan lafiyarki kalau ci ki kara

lafiyar 'yar nan ai ni tausayinki nake ji ke da ki

ka saba cin dadi a gidan mazan da ki ka aura.

Ke dai ina miki addu'a Allah ya kawo miki

wanda za ki huta fiye da su. Nayi dariya na ce

"Haba Baba Ladi, ai wannan addu'ar taki bata

yi ba.

Cewa za ki yi Allah ya kawo mun wanda

zan zauna lafiya a gidan shi zama na din-din-

din wanda zai yi hakuri da halayyata da

dabi' una masu kyau da marasa kyau.

Ni a ganina wannan shi ne mafi alkairi a

gare ni.

Na mike gidan Yaya Auwalu na nufa don

duba matarshi. Ina rike da kwanon da Umma

ta bani na kunun tsamiya da ta dama mata

saboda ganewan da tayi bata cin abinci ya

zauna mata.

Nayi sallama a bakin kofar na shiga. A

kwance na sameta shame-shamc a kasa.

30

Cikin sauri ta gyara zama tana daura

dankwalinta, na ajiye mata kunun ina gaya

mata sakon Umma tana dan murmushi cikin jin

nauyi.

Ban saurare ta ba kicin dinta na shiga na

dauko kofi na tsiyaya mata na mika mata ta

kar6a.

A raina ina tunanin mu'amalla mai sauki

irin wacce ke tsakanin matar Yaya Auwalu da

sirikarta Umma.

Ban jima a gidan ba na fito bayan na gaya

mata zan zo gobe nayi mata kitso, saboda kanta

dake tsefe.

Ina tafe ina tunanin rayuwar da nayi a

gidan Ahmad da mahaifiyarshi, da kuma shi

kanshi.

Da mahaifiyarshi dai kowa ya sani babu

sauki amma da shi wata irin rayuwa da

kowacce mata zata yi mafarkin samu.

Yanzu kuma ko ina zan fada sai Allah, don

kuwa a yanzu ko kwanakin baya da ya kira ni

gaisuwa kawai muka yi ya dan tambaye ni

abubuwa.

31

Saboda jin labarin komawata Makaranta da

yay1, da alama shima ya hakura. Kirana kawai

yake yi saboda mutunci.

Nasiba ita ce kadai yarinyar da nake

mu'amalla da ita a makaranta.

Jininmu ya hadu ne ba don halinmu yazo

daya ba. Nasiba 'yar gaye ce sosai

Irin yan gayun nan da basa kunyar

gayensu. Wadanda yafa gyale ko saka hijabi

bai dame su ba, yar gata ce sosai daga irin

Suturun da take sakawa na fahimci hakan.

Duk da irin bambancin da ke tsakaninmu

muna iin dadin mu'amallar mu don kuwa tana

da matukar kamun kai ba kadan ba.

Mu'amalla ta da ita ya sanya ni na kara jin

dadin karatuna, don kuwa komai tare muke yin

shi.

Amma har da irin sabon da muka yi da juna

ban san komai game da ita ba, kamar yadda ita

ma bata san komai game da ni ba.

Ta dai tambaye ni yarana na ce daya, don

haka ita kallon matar aure take yi mun.

32

Karatu sosai muke yi ba tare da wani wasa

ko kuma yaudarar kai ba, har aka zo rubuta

Jarrabawa.

Bayan yan gwaje-gwajen da aka yi mana

wanda tun daga nan muka fara ganin irin

kokarin mu da kuma ta inda zamu yi gyara.

A komnai kusan muna tafe ne da Nasiba sai

dai a wasu darussan ta fini haka nima a wasu

na fita.

A duk inda dayanmu kuma yafi daya, to a

nan zai rinka koyar da dan uwanshi.

Hakan yayi matukar taimakon mu ba kadan

ba.

Ranar da zamu fara jarrabawa kuwa har

Babana sai da na gayawa, ya taya ni da addu'a

ya kuma jaddada mun a kullum shi din cikin yi

mun addu'a yake.

Zai kuma kara a kan ta da. Na ce to na gode

Baba. Cikin sauki muka yi jarrabawarmu muka

gama ba tare da mun fuskanci wani tsanani ba.

An kuma ce wai Juma'a mai kyau daga

Laraba ake ganeta.

33

Muna rike da hannun juna ranar da muka yi

hutu zamu rabu, Nasiba ta ce amma dai kin san

ba ki da kirki ko?

Cikin murmushi na ce,"Na sani mana

Nasiba."

Ta yamutsa fuska tana kallona, ta ce

"Amsar da za ki ba ni kenan don wulakanci?

Na ce, "To ai kin ga ke ce ki ka fada kin ga

kuma na san ba za ki yi mun karya ba.

Ta ce, "To tunda muke da ke ba ki taba

tunanin ya kamata ki tambaye ni ta inda

gidanmu yake ba, ballantana in saka ran wata

rana zan ganki.

Kullum haduwar Makaranta rabuwar

Makaranta. Ni kuwa a yanzu din nan da nake

ko da ban taba zuwa gidanku ba har kalan

fentin shi na sani. Don kuwa komai yana cikin

zuciyata."

Nan take naji kunyar Nasiba ta kama ni, don

kuwa nasan gaskiyarta kawai ta fada.

Na saka hannu a cikin jakata na dauko biro

da 'yar takarda na ce "Kiyi hakuri Nasiba nayi

kuskure, amma rubuta mun a nan."

34

Ta watso mun wata zabgegiyar harara

sannan tayi tafiyarta ta bar ni a tsaye a wurin.

Sai da nayi wanka naci abinci na wartsake

gajiyata sannan na dauko wayata na rubutawa

Nasiba don gajeren text message.

Kiyi hakuri kawata ban kyauta ba, amma ki

saurare ni zan ba ki surprise.

Miss you so much.

Ranar da aka wayi gari satinmu biyu da

hutu ranar Samahatu ta haifo santalelen yaro.

Ina rike da yaron a hannuna bayan an

sallamo su daga asibiti sun dawo gida bakina

ya ki ufuwa saboda murna.

Shi kuwa Yaya Auwalu sai kaiwa da

kawowa yake yi. Iyayen Samahatu sun so su

dauketa ba a yardan musu ba.

Don haka kullum Inna Hadiza ce mai zuwa.

tayi mata wanka ta yi wa jariri.

Kwanaki uku da yin haihuwar sai ga

Nasiba. Duk da na sanar da ita maganar

haihuwan ban yi zaton zata zo ba.

Rungume juna muka yi cikin murna. Wurin

Umma na fara kaita suka gaisa, na kaita wurin

35

Baba Ladi, sannan na shigar da ita asalin

dakina.

Na ajiye mata abubuwan ci da na sha muna

yar hira tana ta dan kalle-kallenta sannan ta

kalle ni cikin mamaki.

"Yanzun nan Hauwa'u dama ba ki da aure

amma ba ki taba gaya mun ba? Gaskiya ke ba

mutuniyar kirki ba ce."

Na ce, "To kiyi hakuri a yadda dama naso

ki gane kenan. Tayi tsaki ta dauki kunun

ayarta ta fara sha.

Muna 'yar hirarmu tana ciye-ciyenta na

abubuwan da na ajiye mata. Ta ce, "Amma

gaskiya kina da zurfin ciki, koda yake ba zan

ga laifinki ba.

Don kuwa mutanen yanzu ba abin yarda ba

ne, balle kaje kana bude musu sirrinka.

Bayani na yi wa Nasiba na komai game da

ni, zamana a gidan Ishak da kuma Ahmad da

yadda aka yi auren ya mutu.

Tayi shiru jimawa kadan ta ce "Gaskiya

maganin matsalar kenan komawan da ki ka yi

makaranta. Sai ayi ta addu'ar samun salihin

miji a gaba da za ki yi zamanki lafiya da shi."

36

Na ce,"Addu'ata kenan nima."

Zukekiyar riga mai kyau da sabulai hadi da

turmin atamfa 'yar Ingila Nasiba ta bai wa

Samahatu da na kaita ta yi mata barka.

Umma ma tsaraba tayi mata sosai, dangin

kuka, kubewa busassa, daddawa da su citta.

Sannan ta kulle mata yajin daddawan

maijego duka ta ce, ta kai wa mahaifiyarta ta

kuma yi murna sosai.

Babu wanda bai yaba da nutsuwar Nasiba

ba a gidanmu. Munyi shagalin suna sosai da

sosai, yaro ya ci suna Abdurrahman saboda

darajar sunan. Hutunmu ya kare cikin

kankanin lokaci saboda dadin shi da múka ji.

Shiri sosai na sake yi don himmar fuskantar

zangon karatu na biyu, wato second semester a

makaranta.

Duk wani abu da nasan zai taimake ni,

kuma a tanade shi. Sammako nayi saboda

dokin da nake yi na tafi makaranta, duk da

sanin da nayi cewa a yau din rana ce da aka

bude mafi akasarin dalibai ba su zo ba.

Haka nan Malaman ma wasu ba a satin suke

fara shiga aji ba Kan gurin da na saba zama ni

37

da Nasiba naje na karkabe mana na zauna tare

da jawo wani littafi na turanci don ya dan debe

min kewa suna (Jane Eyre) ina karantawa.

Lokaci ya tafi ba kadan ba jifa-jifa kuma ina

dagowa don amsa gaisuwar abokan karatuna

da suke ta shigowa ajin.

Na kalli agogon da ke daure a hannuna don

ganin lokaci saboda ganewan da nayi lokaci ya

tafi.

Karfe takwas ne har da rabi amma Nasiba

bata zo ba. Na dauko wayata kenan da nufin na

kirata sai ga Mallam ya shigo.

Mallam Zakariyya shi ne Malamin da yake

daukanmu GNS wacce madda ce da ta zama

wajibi akan kowanne dalibi na makarantar.

Koda kuwa me ka ke karantawa sanin halin shi

da nayi ne yasa na mayar da wayar na ajiye. Ya

isa gaban allo yana rike da marker a hannunshi

ya rubuta test a jikin allon.

Gabana yayi mummunan faduwa na juya

don kallon sauran 'yan tsirarun ajin suma sai

zazzare idanu suke yi alamar bani kadai ba ce a

cikin rudani.

38

Sai dai babu wanda ya tanka. Ya rubuta

tambayoyin shi yaja gefe yana nade da

hannayenshi a kirji yayin da yake binmu da

kallo.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login