Showing 12001 words to 15000 words out of 23627 words

Chapter 5 - MAI DAKI (4) Book Complete By Hafsat C Sodangi.docx

22 Jan 2026

26

kasa sakin jiki

da irin mu'amallar Mallam da matarshi.

Na sani tare na same su amma da sai su

rinka bari idan bana nan suyi abinsu.

Gyara zamana nayi a kan kujera na rufe ido

nayi kamar ina barci ne. zuwa can naji ya kira

sunana.

Shiru nayi ban amsa ba. Amina ya kamata

kije ki kwanta dare fa ya fara yi, goma ta wuce.

Shiru tayi bata amsa ba zuwa can na dan ji

shishikar kuka shi kuma yana cewa menene

kuma? Me aka yi miki na kuka?

To darling yaya ba zan yi kuka ba don Allah

wai har an yi lokacin da ni zaka kore ni a

dakinka saboda ka matsu da wata ni kuma na

isheka ko?"

"Haba Amina, wannan wace irin magana ki

ke yi haka? Kina so ki tsokalo magana ne

kawai.

Idan kinga ba za ki tafi ba zauna mu kwana

duka a nan. Magana ta kare.

74

"Hauwa'u." Ya kara kirana. Shiru na sake

yi, sai da ya kara daga murya na amsa tare da

gyara zama ina kallonshi.

"Shiga daki ki kwanta." Abinda nake ta jira

kenan, don haka ban tsaya bata lokaci ba na

mike na nufi hanyar fita.

Ya ce, Ina za ki je? Na juyo ina kallonshi ga

daki nan shiga ki kwanta."

Wucewa nayi na shiga daya daga cikin

dakunan kwananshi biyu da ke falon.

Na gyara na kwanta sai dai ba barci nayi ba.

Haka nan sama-sama ina jiwo maganar ban dai

san me suke yi ba.

An kusa awa guda sai naga shigowar shi

ban dai motsa ba har da maganar da yayi mun

don ya gani ko nayi barci.

Washegari da asuba yana dawowa daga

sallah tun zuwa na ban taba lekawa ba.

Babba ne sosai don kuwa ya kai girman

daki, haka nan zagaye yake da tiles kasa da

jikin bango.

A gefen sink an saka kabinet bango zuwa

bango ga gas cooker freezer da na'urorin girki.

75

Ya kalle ni ina so ne za ki fara yin girki

daga safiyar yau tunda kinga ai Amina tayi

miki na kwanakin ukun da ki ka yi har gashi

tayi na jiya ko?

Na ce haka ne, don haka ina so ko shayi ne

ki hada a sha da rana sai a yi abinci na ce to.

Kamar yadda ya fada hakan nayi sai dai na

dada da soyayyen kwai tunda da biredi za a sha

shayin.

Yana tsaye yana saka links din rigarshi ni

kuma ina goge mishi takalman da zai sa

maganar makarantata tana cina a rai.

Amma gagara yi mishi maganar. Ya gama

shirin shi zai tafi ya ce, "Kiyi wa Amina

magana zata nuna miki komai na kayan

amfani."

Na ce, To. Har ya juya sai ya dawo "Kina

da magana ne? kamar nayi shiru sai na kasaa

na ce eh.

Ya ce, "To menene? Na ce, Ta game da

makarantana ne. Ya ce, Ban manta ba, sai da

nayi nufin kiyi sati biyu ne sai ranar Monday ki

fara zuwa.

76

Amma idan kinga hakan bai yi miki ba ki

shirya gobe ki fara zuwa.

Na dawo dakin nashi nayi mishi

kyakkyawan gyara na hada kayan wankin

dakin.

Sannan na nufi kicin don nasan dakina baya

bukatar gyara. Sai da na gama gyaran kicin din

sannan na fito na samu Amina a dakinta.

Tana can ciki, don haka a falo na tsaya nayi

sallama. Ta fito cikin murmushi.

"A'a, Amarya ta fito ko ai darling yayi mun

magana kan ya kamata na huta haka kema ki

shiga kicin din, shekaru bakwai ai ba sawa, ba

ne.

Kullum fa aikin kenan da safe kana kicin da

rana haka da daddare kuma baka huta ba. Ai

kin ga kwana biyu ai nima na kan samu barci.

Don jiya har ce mun yayi na kara dan nauyi

alamar nayi kiba."

Na ce, "Haka ne. Ya ce, Nazo wurin ki ki

nuna mun abubuwan amfani."

Ta fito ta shiga kicin din tana nuna mun

inda abubuwan suke. Ta juya ta fita na kasa

hassala komai don bacin rai.

77

Me take nufi da maganganun da tayi mun.

na dan kokarta na fara aikina.

Dafa duka nayi da taji hadin kayan lambu

da karas da hanta, sannan nayi lemon ginger na

hada duka na gama cikin kankanin lokaci.

Don haka nayi wanka na gyara jikina na

kammala komai a wajen shi kamar yadda aka

saba.

Ba a wani dade ba naji dawowarshi na mike

na shiga falon, amma har Amina ta riga ni ta

tsiyaya mishi lemon jinjar tana ba shi a kofi.

Raina ya sosu amma sai na shanye na

karasa tare da yi mishi barka da zuwa.

Na gyara zama ina zuba mishi abincin na

mika mishi ya karba ya fara ci, ita ma Aminan

tana ci tana magana.

Kaga cin abincin yan Jami'a, wannan

hade-hade ai dole yayi dadi ko ya ki don kuwa

zakin abinda ke ciki kawai ya isa.

Kamar yadda ban ce ba haka shima ya gama

cin abincin shi ya koma wurin aiki, nima na

tattara wurin sannan na fitO na samu yara sun

dawo.

78

Na basu abincin sannan na dora na dare,

tuwo nayi miyar kuka.

Ana gobe zan koma makaranta. Mallam ya

zauna damu a falon shi Amina Hauwa'u zata

koma Makaranta gobe.

Don haka ina so ki rinka yin abincin rana

kullum in yaso ita sai ta rinka yin na dare.

Bata musa ba haka nan ni ga wurina sauki

na samu, don haka shiri sosa nayi da sassafe

muka fita tare zuwa Makaranta.

Yan ajinmu kowa da abinda yake fada

akan canzawar da nayi, ballantana Nasiba da

ke ta bina da kallo.

Ta dai gaji ta ce, "Kai mu ma dai bari muyi

auren nan mu ji." Na ce, "Kyaji dai da shi."

Kullum da safe tare muke tafiya Makaranta

mu kuma dawo tare. Idan muka dawo kuma to

zan zo na samu Amina tayi abincinta na rana.

Don haka ni kuma idan na dan huta sai na

shiga kicin nayi na dare.

Ban taba sawa Amina ido a kan harkarta da

mijinta ba. Don kuwa ranar kwananta ina gama

cin abincina nake tashi na tafi dakina nayi

harkokin gabana.

79

Amma idan kwanana ne to sai ta kai sha

dayan dare, idan ba ce mata yayi zai kwanta

ba.

Haka nan idan ranar kwananta ne ko da

nake yin abincin dare to ita nake mikawa bana

cewa don nayi abincin sai na zuba mishi da

hannuna.

Ita kuwa ko ni ce nayi abinci ranar kwanana

to idan ban yi da gaske ba sai ta zuba ta mika

mishi, tana tambayarshi abubuwan da yake so.

Nayi ta kokarin daurewa akan abin, amma

ta kai ma daga shi har ita sun kure ni.

Don haka yau da na gama abinci kai musu

nayi falon na baiwa kowa a gidan nashi na

debo nawa na dawo dakina na zauna naci na

koshi.

Na dauko assignment din da nake dashi na

fara yi. Wajejen karfe tara sai gashi ya shigo

dakin ya nemi wuri kusa da ni ya zauna.

Lafiya ki ka dawo nan?"

Na ce, "Lafiya kalau, ina dai da abin yi ne."

Ya ce, "To ai da sai ki zo muje can kiyi

abinda za ki yin." Na ce, "Ai ina son nutsuwa

ne sosai."

80

"Kina so ki ce mun idan kina tare da ni ba

ki da nutsuwa?

Na ce, "Ni fa ba haka nake nufi ba, amma

ka duba ka gani fa lissafi ne kashi uku cikin

hudun aikin.

Haka dai ya hakura ya bar ni ya tafi.

Washegari kuwa naci abinci a falo sai dai

ban wani bata lokaci ba na mike na dawo

dakina.

Koda kwana ya juya kan Amina ma ban

tsaya ba ina gama cin abinci nake dawowa

dakina.

Idan ya tambaye ni na ce kasan jarrabawata

kusa ina da bukatar samun lokaci don karatu.

Sai dai ban sani ba ko abin ya fara gundurar

shi ne. da wurwuri na gama aikina na kammala

komai a yadda muka saba na dauko nawa na

dawo dakina na zauna.

Zan fara ci sai gashi ya shigo, "Tashi ki

wuce muje. 99 Na kalle shi sai dai ban musa

mishi ba don banga alamar zan iya yin hakan

ba.

81

Saboda yanayin da na gani a tare dashi

Muna shiga falon Amina tana zaune tayi baje-

baje ta sheka kwalliya sai kyalli take yi.

Ta kalle ni tayi 'yar dariya ta ce, "Hauwa 'u

kenan 'yar lelen darling to ke in banda abin ki

kin san darling ya saba cin abinci a nan don kin

yi girki.

Ki dauki naki kin tafi ai kin san ba zai sa ya

dauki nashi ya biki ba takamar ke ki ka yi.

Ban ce mata komai ba shima bai ce ba sai

dai maganar ta kara 6ata mun rai.

Nemi wuri ki zauna ban kuma yarda daga

yau ki kara daukan abincinki ki tafi wani wuri

kici ba.

Ban wani ci abincin ba, shima kuma hirar

yau ba wani sosai yake amsata ba tara da rabi

nayi na mike da nufin zuwa na kwanta.

Ya ce, Ina za ki na ce zan kwanta ya ce ga

dakinan na dan yi jim saboda ko kadan bana

jin dadin raina na ce ina so ne na yi

assignment.

Ya ce, Gobe kiyi. Dawowa nayi na wuce shi

na shiga dakin barcin shi ya kwanta

82

Bai shigo ba sai wajen goma da ashirin.

Daidai inda nasa kaina a filo yazo ya tsaya ya

kira sunana na amsa ya ce tashi ki zauna.

Menene damuwarki? Ya tambaye ni bayan

shima ya zauna a kan wani madaidaicin stool

muna fuskantar juna.

Na ce, Babu. Ya ce akwai gaya mun kawa

don na san kina da ita. Nayi shiru ban ce komai

ba.

Haba Hauwa'u idan nayi miki wani abu ki

fada mun don na gyara idan kuma wani ne sai

na dauki matakin da ya dace akai amma 1dan

ba ki fada mun ba wa za ki fada ma?

Ba zamana kike yi ba. Ba zan so na rinka

ganin ki cikin bacin rai ba abin kuma da ke

faruwa kenan kwana biyun nan maganganun da

yake yi mun su ne suka sani fara kuka saboda

nauyin da kirjina yayi mun.

Sai da nayi kukana na share hawaye sannan

ya ce "Kiyi hakuri amma ban san na bata miki

rai haka ba.

Ya mike ya dauko robar ruwan sanyi ya

miko mun, ban musa bà na karba na

83

kwalkwala na gyara zan kwanta tare da jan

bargo zan kwanta.

Yana zaune a inda yake ya ce "Idan ki ka y1

mun haka kin yi mun adalci? A hankali na ce

"Me nayi maka na rashin adalci?

Ya ce, "Ba ki sani ba? ya ce, Yaushe rabon

ki da kwana a dakin nan? Kin kusa kwana

goma.

Na kyale ki ne saboda bana son takura miki,

amma ke banga haka a tare da ke ba. A yanzu

kuma da na tirsasa ki kin ja bargo kin rufa.

Tashi kiyi min bayanin abinda ki ke so zan

yi miki, amma bana son ki rinka kokarin da

karfi sai kin tauye mun hakkina da ke kanki.

Danne tawa damuwar nayi na biya mishi

tashi bukatar. Zazzabin da na tashi dashi shi ne

yayi dalilin da muka kusa makara.

Duk da ban tsaya yin wani abu ba baya ga

shayin da na dafa.

Daidai lokacin da muka yi break sai ga

wayarshi. Na kalli Nasiba na ce, Ki raka ni

ofishin Mallam yana kirana.

84

Ta ce, A'a ke dai je ki nasan abinda kiran

yake nufi, sai kuma kawai ya ganni sokai-sokai

na rakaki.

Na juya na barta a friends joint na nufi

ofishin shi. Na samu dalibai da yawa anmma sai

na nemi wuri na zauna a can gefe saboda sanin

da nayi ofishin ba ya rabo da dalibai masuu

matsala.

Don shi ne Dean of students affairs, yana

sallamar na ciki ya kira sakatariyar shi ya ce

mata kada wani ya sake shigowa.

Sannan ya dawo ya ce Yaya jikin naki? Na

ce da sauki. To me zan kawo miki? Na ce,

ruwa kawai.

Ya miko mun ruwan sannan ya zauna a kan

doguwar kujerar da nake zaune a kai ya mannu

da jikina.

Na dan yi kokarin matsawa don kuwa

kunyar Mallam kan kama ni a irin wadannan

lokutan.

Shima matsowa ya sake yi na dan yi

murmushi ya ce, "A to kya yi dariya dai kema

me yasa ki ke guduna?

85

A hankali nayi magana na ce,"Bana

gudunka. Ya ce, "Kina yi mana koda yake na

fahimci laifi nayi miki shi yasa nake so ki gaya

mun laifin.

Na rasa yadda zan yi nayi mishi wata

magana. Kada kiji kunyar gaya mun

matsalarki.

Ganewan da nayi ba zan iya kaucewa ba

yasa na ce, Ni dai kawai na fi so na rinka zama

a dakina ne.

Ya ce, Zan bar ki ki rinka zama a dakinki

idan kin gaya mun dalili. Na ce, dalilin kenan

saboda karatuna.

Ya ce, Ban yarda ba, wannan ba dalili ba ne,

don haka ban yarda da zaman daki ba, tashi ki

bani madara a fridge.

Na mike na isa wurin fndge din na dauko

hade da tumblan na tsiyaya na mika mishi, ya

zuba mun ido yana kallona.

Na dan kawar da kaina gefe. Yasa hannu ya

riko hannuna da kofin gaba daya ya kai

bakinshi. Sai da ya shanye madarar sannan ya

sake hannuna na ajiye kofin.

86

Ya ce, Koyi hidimar mijinki. Ki kula da

abubuwan da yake so da dabi'unshi nunawa na

kusa dake cewa abinda yake yi baya baki

haushi.

Don za ki yi wanda yafi haka. Kina da kyau

kina da kuruciya, baya ga haka Allah yayi miki

wasu baiwa da kema ba ki san da su ba.

oUwa uba kuma mijinki yana sonki. Kada ki

bar wa wata mijinki saboda zafin kishi.

Kuma don kina jin haushin wani abu ba zai

sa na canza dabi'ata ta zama da ku ba a

kullum.

er Juyowa nayi na kalle shi saboda abubuwan

da yake fada. Ya ce, Eh matsalarki kenan ko ba

haka ba ne?

Na ce, Ni ba haka ba ne, na ce maka bani da

matsala. Ya dan yi dariya ya ce, To naji ba ki

da matsala.

Na mike da niyyar tafiya, don ganin lokaci

ya kure na break din mu, na dauki tumblan da

robar zan mayar, shima ya mike ya biyo ni.

Ina ajiyewa na juyo ya rike ni tare da

mannani jikin bango yasa hannu ya zare

hijabin da ke jikina.

87

Na dan fara kokarin yin magana amma bal

bar ni ba. Na fara kokarin zamewa ya dauke ni

ya ajiye ni a kan makeken teburin da ke

tsakiyar office din.

Da kyar naja jikina na koma kan kujerar da

na baro na kifa kaina. Na kasa komawa kusa da

shi na dauki hijabina. Na kuma kasa kallon shi.

Ya taso ya zauna kusa da ni tare da jawo ni

jikinshi nayi saurin cewa zan koma aji fa

kuma...ya ce, kuma me?

Kunya tana da kyau a addini, amma taki

tayi yawa Hauwa'u, ki daure ki dan rage

saboda ni ki taimake ni kema kuma ki taimaki

kanki.

Da na dawo na zauna sai na fahimci gaskiya

kawai ya gaya mun, kishi shi ne abinda yafi

kuntata min.

Don haka ya zama dole nayi koyi da

shawarar da ya bani. Shiri sosai nayi ranar da

na karbi girkina nayi kayatacciyar kwalliya.

Na shiga dakin shi na fitar da duk wani

abinda bai yi mun ba, na sake shimfidu na

feshe shi da turare.

88

Ina kammala abinci kuwa na hada komai

na zauna zan fara zuba abinci sai Amina ta

dauko plate din shi zata zuba mishi kamar

yadda ta saba.

Na mika hannu da niyyar karba, ta kalle ni

ai zan zuba mishi ne, na ce eh na sani amma ci

naki kawai na hutar da ke.

Ta dan tabe baki tare da cewa, ai shi kenan

na zuba mishi na mika mishi, sannan na zuba

mishi abin sha na ajiye a kusa da shi.

Sannan na zuba nawa na fara ci. Duk motsin

da zai yi idona na kanshi na kankane, don haka

yau ko doguwar hira ba ayi ba.

Tun ina yi ina dan jin kunyar abubuwa har

na zake, sai kuma na gane da gaske abinda ys

takura mun kenan.

Shirye-shiryen jarrabawarmu ya kankama

gadan-gadan, don kuwa a gobe ne ma zamu

fara.

Zama tsakanina da Amina ya canza gaba

daya, don kuwa sai na gaisheta sau uku kafin ta

amsa mun sau daya.

89

Ban kuma taba fasawa ba. Ko wurin cin

abinci muka hadu sai takai ta kawo ne magana

ke hada mu.

Idan bata ga dama ba kuwa ko nayi mata

bata amsawa. Ta daina shisshigin zuba mishi

abinci ranar girkina, ko shisshige mishi da take

yi.

Shirin jarrabawa ta bata hana ni hidima da

mijina ba, don kuwa a yanzu ne ma nake jina

na fara auren.

Na gama hada abinci a falo na fara zuba

mishi salad saboda azumin da yayi.

Ya fara ci na kai hannu zan dauki cokali sai

naga ta rike, na ce barı mana na gama zuba

mishi sai na baki.

Kan na ankara sai kawai naga ta fauce shi a

hannuna ta ce, To duk maitakarki sai na zuba

nawa, jarrababbiya kawai.

Bude baki nayi galala ina kallonta, shi kuma

cikin bacin rai ya ce, Yaya haka? Meye haka

kuma daga magana sai ki zage ta? To bana so.

Eh mana ai dole ka ce ba ka so sai kawai ta

fashe da kuka. Muna zaman zamanmu ka

dauko masifa ka kawo mun cikin gida.

90

Duk abubuwan da take yi mun kana gani ba

ka ce komai ba, saboda ba haka kawai ta barka

ba, da haka muke?

Ta shiga tsakaninmu ko kallon arziki baka

1ya yi mun sai idan bata nan har ta kai ma zata

wulakantani a gabanka, kuma ka goyi bayanta.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login