Showing 6001 words to 9000 words out of 23627 words

Chapter 3 - MAI DAKI (4) Book Complete By Hafsat C Sodangi.docx

22 Jan 2026

23

/>
Na yago takarda na rubuta suna, course

(madda), department da kuma matriculation

no, nayi gaggawan rubuta abinda na sani daidai

gwargwado.

Sannan na jawo wata takardar duk da

faduwar gaban da nake yi baisa na fasa abinda

nayi niyya ba.

Nasiba na rubutama duk kuwa da sanin

halin shi da nayi. Muna gamawa ya karba

sannan yayi mana dan karatun da zai yi mana

ya fita.

Ban ko tsaya jiran wani darasin ba, fitowa

nayi daga makaranta na wuce gidan su Nasiba.

Babban gida ne sosai irin na masu kudin da,

sai dai gini ne na bulo amma sashe-sashe.

A yadda Nasiba kuma ta gaya mun to a

gidan nasu kaf dinshi ita ce 'yar autansu.

Matan Babanta hudu ne don haka Yayu ne

da ita maza da mata masu yawan gaske.

39

Wani yaro ne ya shigar dani har dakin

Nasiba kamar yadda nayi zato kuwa bata jin

dadi ne.

Bata yi zaton ganina ba sai dai taji jiki don

gaba daya ta zube. Ta kokarta ta wartsake har

ta karya saboda lokacin da naje bata ko karya

ba.

Tayi wanka sannan ta kai ni wurin

mahaifiyarta. Maman Nasiba Hajiya Tani

dattijuwa ce sosai, don kuwa zata kai shekaru

sittin da biyar zuwa saba'in amma kuma das da

ita.

Da karfinta babu wani alamar da zai nuna

cewa shekaru sun hau mata ka.

Na durkusa ina gaisheta tana amsawa cikin

fara'arta. Yayinda Nasiba take gabatar mata da

ni. Ta tambaye ni karatu da iyayena na bata

amsar komai lafiya.

Ban wani zauna ba na mike da nufin tafiya,

Hajiyar Nasiba tayi mun alheri sosai, na fito

bayan na jaddadawa Nasiba lallai tayi kokarin

zuwa makaranta gobe saboda tsoratar da nayi

da abinda Mallam Zakariyya yayi mana.

40

Ta kuma yarda don kuwa a washegari har

sai da ta riga ni. Karatu ya kankama sosai don

kuwa muna cikin sati na uku ne a cikin wannan

zangon.

Muna zaune a a friends joinrt inda mafi

akasarin lokaci idan anyi break sannan ba mu

da abin yi a wurin muke zama.

Hira muke yi cikin nishadi da wasu daga

cikin 'yanmatan makarantar mu.

Kowa yana nashi korafin ne a kan yadda

yanmatan Jami'a suke bai wa Malamai

kawunansu, wanda kuma hakan shi ne ke kara

lalata mana al'amura.

Yake rage mana mutunci suke kuma ganin

mu a araha banza. Wani yaro ne ya iso wurin

da alamar gajiya a tare da shi.

Watakila saboda sassarfar da yayi don

isowa wurin da muke zaune.

"Hauwa'u kije in ji Mallam Zakariyya."

Abinda ya fada kenan, a lokacin da ya gama

gaishemnu.

Gaba dayanmu muka zuba mishi idanu

saboda yadda abin yazo mana kwatsam. Take

alamar tsoro ya bayyana a idona, sai dai kafin

41

na samu damar tambayar shi har Nasiba ta riga

ni.

"Lafiya yake nemanta?"

Abinda ta ce mishi kenan, sai dai a

maimakon ya bata amsa dariya yayi ya ce.

"Ka ji Malama Nasiba, ana tambayar

tsakanin Malamin Jami'a ne da kuma

dalibarsa.

Juyawa yayi ya yi tafiyarshi, bayan ya ce

yana fa jiran ki don kada ya ce ban fada miki

ba."

Da ni da Nasiba muka mike don zuwa kiran

Mallam Zakariyya, ni dai gabana sai faduwa

yake yi abinda yasa shi kirana.

Don kuwa ni ban ma san ya sanni ba, haka

nan ban tuna wani laifi da nayi mishi ba.

Har muka isa kofar ofishin nashi babu

wanda ya tankawa wani a tsakaninmu. Na taba

kofar a hankali naji an ce shigo.

Nayi kyakkyawar sallamata bayan na

karanta addu'o'in neman tsari.

"Ina wuni Mallam?"

42

Yana zaune a kan kujerar ofishin nashi yana

duba wata zungureriyar takarda mai dauke da

zanen map (Taswira).

Sai da ya gama nadeta sannan ya samu

daman amsa mun gaisuwar da nayi mishi, ya

dago kanshi yana kallona tare da dan

Jujjuyawa a kan kujerar tashi.

"A gwajin farko da nayi muku na ranar da

aka dawo daga hutu akwai karin takarda daya

da ta hau kan adadin yawan daliban da ke ajin

a wannan ranar.

A iyakacin binciken da nayi sai na fahimci

kece ki ka rubutawa kawarki saboda rashin

tarbiyya da sanin ka idar neman ilimi.

Don haka zan yi amfani da ke don ki

zamanwa sauran daliban ajinku darasi a kan

ganganci irin wannan koda kuma a nan gaba

wani zai yi kuskuren yi to ba zai zama a kaina

ba.

Don kuwa ni mutum ne mai bin komai nawa

bisa tsara da bin ka'ida. Fita ki bani wuri."

Na fito jikina a sanyaye na samu Nasiba a

tsaye a waje tana jirana saboda kin shiga da

tayi.

43

Ta ce, "Lafiya dai ko? Na ce, "Lafiya

kalau. Ban yi niyyar gaya mata abinda ya faru

ba, don kada tayi tunanin ita ce sanadi.

Duk kuwa da rokona da tayi tayi, har taj1

haushi ta kyale ni.

Babu iin tunanin da ban yi ba a kan

matakin da Mallam Zakariyya yake nufin

dauka a kaina.

Shin zai sa ni na maimaita maddar ne ko

kuwa yaya? Maimaita madda irin wannan mai

matukar muhimmanci ba karamin abu ba ne.

Ya zama dole na je na ba shi hakuri.

Washegari sanin da nayi muna da shi da

safe yasa nayi sammakon tafiya. Sai da ya

gama da mu ya fita sannan na mike na bishi

don nayi mishi magana.

Ina shiga ofis din nashi ya dago kai ya kalle

ni fuskarshi a murtuke.

"Yaya lafiya dai ko?"

Na ce, "Eh lafiya Mallam."

Ya ce, "To na kira ki ne?" Yayi tambayar

cikin daga hannayenshi alamar jaddada

tambayar tashi.

44

Na ce, "A'a Mallam don Allah nazo ne don

na baka hakuri bisa kuskuren..."

Kan na karasa sai kawai naji ya ce "fitar

mun a office."

Sum-sum na wuce na fita na dawo aji jikina

kamar an bi gabobina an bubbuge su.

Na samu Nasiba a ajin bata ce mun komai

ba, nima ban ce mata ba, ita dai da alama fushi

tayi don kuwa taga lokacin da na bi bayan

Mallam Zakariyya.

"Wai me ki ke nufi ne da wannan

wulakancin da ki ke yi mun? ina binki ina

tambayarki abu kina wani daddaure rai kina

bata fuska?"

Na kalleta na ce, "Ba fa daure rai nake yi

ba." Ta tabe baki ta ce, "Kya dai ji da shi, ni

nasan Mallam Zakariyya ba zai kira ki don ya

nemi lalacewa da ke ba.

Don kowa ya shaide shi a makarantar nan.

Ni nasan da abinda ya faru amma kiyi mun

bayani kin ki, ai kuma sai kiyi ta yi."

Haka na wuni sukuku babu lakka a jikina.

Da na dawo gida ma Umma sai da ta gane. Ita

kam nayi mata bayanin komai.

45

Ta ce, "To ai sai kiyi hakuri kawai ki roki

Allah ya sassauta fushin nashi idan kuma ya

saki kin maimaita ma ai shi kenan tunda ba

karatun ba ne gaba daya za a fadi ko?

Idan badi tazo da rai sai ki sake rubutawa ai,

shekara kwana ne ga mai rai. Allah kuma yasa

hakan ya fiye miki alheri."

To na dan ji dadin bayanin Umma, wanda

hakan yayi matukar sani na dan wartsake.

Duk da sanin tsakanina da Mallam

Zakariyya da nayi bai sa na daina halattar

darasin shi ba.

E Haka nan na kara dagewa sosai da sosai ba

ma akan darasin shi ba kawai har a kan saura.

Kamar yadda ya saba na bayar da test ba

tare da anyi zato ba yau ma haka yayi daidai

gwargwado, kuma na amsa tare da yin bayani

filla-filla.

Kwanaki biyu bayan nan ya aiko da

takardar yin gwajin, abin mamakin shi ne,

mutum biyu ne suka ci, sha takwas a ajin gaba

dayanshi, daga wani yaro namiji sai ni a mata.

Nade takardar nayi na cusa a jakata saboda

zagaye ni da aka yi don tabbatarwa yayin da

46

wadanda abin ya basu haushi suka fara haba!

Ai dama biri yayi kama da mutum.

Don kuwa ai yanzu bini-bini sai ka ganta a

office dinshi.

Nasiba ta kalle ni, bayan mun fito ta ce, "Ni

me ke tsakaninki da Mallam Zakariyya ne?

wannan shi ne karo na uku da nake tambayarki.

Kuma ba zan sake ba daga wannan karon."

Na dan yi murmushi nayi mata bayanin duk

abinda ya faru, har zuwa yau.

Ta ce, Ikon Allah, to Allah dai yasa ba

yayi miki makin ba ne kawai."

Na ce, "Nima tsoron da nake ta ji kenan."

Nayi iyakacin taka tsan-tsan kan al'amurana

da sauran Malamai gaba daya, ba ma Mallam

Zakariyya shi kadai ba.

Har aka yi jarrabawarmu ta wannan karon

wacce da ni da Nasiba muke sa rai da

kyakkyawan sakamakon.

Rayuwata tana tafiya mun yadda ya kamata.

Na cire komai cikin raina. Ahmad, Ishak da

danshi duka burina kullum na ga na kammala

karatuna ne.

47

Na karbi sakamakona cikin nasára na tafi

bautar kasa sannan na zama Malamar makaranta.

Burina kenan, to amma anya hakan zai yiwu

kuwa? Har a yanzu ina da wajen shekaru biyu

ne a gaba kafin na gama makaranta.

Amma ban taba sauraron wani da sunan

yazo zance wurina ba, don gudun samun

matsala a wurin 1yayena.

To suma kuma har yanzu ba su ce mun

komai ba. A yanzu hutunmu ya kare mun shiga

shekara ta uku ne.

Zan iya cewa a ajinmu gaba daya babu

mace da ta fini fice da hazaka, don haka

Malamai gaba daya sun sanni don hazakata.

Wayewar garin yau Asabar ce, don haka

duk kokarina na ganin na gama ayyukana ne

da wuri na tafi gidan Yaya Auwalu wuni.

Sai dai kan na kai ga gamawa Babana ya

shigo gidan.

"Idan kin gama ayyukanki kizo ki same ni."

Na ce,To. Ba tare da wata fargaba ba.

Na kammala cikin sauri na samu Babana

kamar yadda ya umurce ni.

48

Ina shiga dakin na kara nutsuwa saboda

ganewar da nayi neman da yake yi mun mai

muhimmanci ne.

Umma tana zaune a can gefe da alama kuma

wata maganar suke yi.

Na durkusa a gefe na ce, "Gani Baba. Ya

ce, "Zama za ki yi da kyau."

Na gyara zaman da nayi ta hanyar zama a

kan tabarmar da ke shimfide a tsakar dakin.

"Na kira ki ne saboda a ganin da nake miki

a yanzu to ya kamata ace kina da cikakken

hankali da kuma tunanin irin na manya.

Haka nan ko baya ga haka addini ya baki

yanci na kanki, a duk lokacin da wata bukata

ko hukunci da ya dangance ki kai tsaye.

Kuma ko da nake uba wato Mahaifi a gare

ki, nayi miki alkawari zan yi iyakacin kokarina

don ganin ban tauyeki na tilasta miki wani abu

ba.

Akwai wasu mutane da suka zo suka same

ni kan na basu izini na neman aurenki, kamar

kimanin watanni biyu kenan, ban yardar musu

ba ne a wannan lokacin saboda kokarin da nayi

49

na ganin nayi kyakkyawan bincike a kan shi

mutumin.

A iyakacin abinda naji na kuma gani a

game dashi ban samu wani mugun abu ko

mummunan abu ba.

Mutum ne na gari abinda mutane suka fada

kenan a game da shi.

To a jiya da daddare sai ga wani aiken ya

sake yi duk dai akan maganar ne na kuma

yardar musu amma hakan ba yana nufin

maganar aure ya tabbata ba ne.

Don ba zan tilasta miki ba, don kuwa a

shekaru uku zuwa hudun da kika yi a gida

banga wani laifi ko mugun abu da ki ka yi ba.

Wanda zai sa na tilasta ki yin aure a wannan

lokacin ba. Amma duk da haka ina so ki san

shi aure hijabi ne a wurin 'ya mace, shi ne ke

kara mata martaba, kima da kuma mutunci.

Shiru nayi cikin wani irin yanayi da

zurfaffen tunani. Abin da ban taba zaton zai zo

mun a yanzu ba kenan, wato maganar aure.

Wandakuma hakan yana daga cikin

manyan dalilan da suka hana ni sauraron kowa

50

Menene zai biyo baya kenan a yanzu

Tunanina ya dawo a daidai lokacin da naji

Babana yana cewa zai zo a cikin kwanakin nan

don ku daidaita.

Na ce, "A'a Baba ba sai ya zo ba ma, idan

yayi maka shi kenan."

Babana ya ji dadin maganar da nayi ba

kadan ba, amma duk da haka sai ya ce "A'a ai

zuwan nashi yana da kyau, don ku san juna."

Na tashi na dawo dakina jikina a sanyaye.

Sanya mun albarkar da Babana yayi ta yi bai sa

na wartsake ba.

Baba Ladi ta kalle ni ta ce, "O' oh maganar

auren ne ta mayar da ke haka? Ko gidan Yaya

Auwalun da nayi niyyar zuwa kasawa nayi.

Aikin da na zaba yi na gida kuwa Umma ko

saurarona a kai bata yi ba.

Al'amuran baya sai suka fara dawo mun.

"To shi kenan shi kuma wannan auren idan

nayi shi menene zai zamo nashi matsalar? Don

kuwa a yanzu sai na fahimci cewa babu wata

mata da take zaune a dakin mijinta ba tare da

tayi hakuri da wasu matsaloli ba sai dai kawai

na wasu yafi na wasu.

51

Haka nan na wasu yayi sanadin mutuwar

aurensu yayinda na wasu kuma ake ta ci gaba

da fafatawa.

Ba hakuri ko rashin hakuri ba ne yake kashe

wa mata aure, sai dai kawai kowacce mace da

nata kaddarar.

Don kuwa sai kaga wata matar masifaffiya

ta fitini kowa dangi da shi kanshi mijin ba

dadinta ya ji ba. Amma auren na nan ana zaune

a haka saboda kaddarar ta ba ta aure-aure ba

ce.

Haka nan wasu matan kuma sai ka same su

masu matukar hakuri, amma wasu 'yan dalilai

da ba su kai sun kawo ba sun zamo dalilin

rabuwar nasu auren.

Ni kam a kafin zuwan wannan rana fatana

daban, haka nan hankalina a kwance yake.

Haka nan nayi kyau na sake murjewa na zama

cikakkiyar mace.

Wanda kana ganina ka san ina da

watacciyar nutsuwa da kwanciyar hankali.

To amma tunda Babana yayi mun wannan

maganar sai naji gabana ya fadi, don maganar

aure a yanzu yana tsoratar da ni.

52

A take sai na fahimci dai wato ita 'ya mace

da zarar ta gima ta kai munzalin aure sai ta

shiga cikin wani yanayi.

Idan tayi auren matsaloli idan bata yi ba ma

hankalinta ba kwanciya yayi ba.

Don kuwa ita a lokacin burinta bai wuce na

auren ba, haka nan mutanen gari ba barinta za

su yi da zantuttuka ba.

Tsawon daren nan ban runtsa ba tunani

kawai barkatai a cikin raina.

Baba Ladi da bata barci mai nisa saboda

kusur-kusur dinta da kuma sabo da tashin

nafilar dare har tayi ta gama idona biyu, ban

kuma tashi ba saboda ina hutun sallah.

Sai dai duk da haka kwana nayi addu'o'i

ciki da bakina da kuma zuciyata.

Ban samu na runtsa ba sai bayan da aka yi

sallar asubah. Wajen karfe takwas da kwata na

tashi na fito tsakar gida da nufin nayi wanka na

kama ayyukana, sai na samu Umma ta gama.

Na nemi wurina zauna ina karyawa ita kuma

Umma tana tankade garin alkama da zata yi

tuwo dashi sai kawai ga sallama.

"Wai ana sallama da Hauwa'u."

53

Cikin sauri na dago kai na kalli yaron,

sannan na kalli Umma. Tankadenta take yi ko

kallona bata yi ba.

Da wannan irin safiyar kuma kira haka ko

karyawa ban yi ba. Sai dai duk da abinda na

fada ban fasa tashi ba.

Don kuwa ba sai an ce mun ga mai kiran ba,

mutumin da Babana yayi mun magana a kanshi

ne.

After dress na dauko na dora a kan riga da

wando na material da ke jikina na mutsuka

hoda don ko hodar ban shafa ba da na fito

wanka.

Na dosa hanyar fita kofar gida sai dai a

daidai nan ne naji wani irin mummunan

faduwar gaba take na fara jero addu'o'i ina

maimaitawa.

Ina kuma fata duk wanda zan gani yayi mun

a cikin raina kada na samu matsala ya kuma

zamo mai alkhairi a gare ni.

Don kuwa bana fata a kan maganar aurena

Babana ya sake bacin rai.

Na isa daidai inda yake tsaye ya jingina da

mota. Daga bayanshi na fito.

54

Don haka na dan kare mishi kallo. Dogo ne

dan siriri yana kuma sanye da kaftani masu

ruwan kasa.

"Salamu alaikum! "

Nayi mnishi sallama daidai na karasa inda

yake, me zan gani? Amsawar da zai yi tare da

juyowa sai kawai muka yi ido hudu da Mallam

Zakariyya.

Shi kanshi ya gane kaduwar da nayi da na

ganshi. Murmushi yayi abinda ban taba sanin

ya iya ba.

"Malama Hauwa'u kina nan lafiya ko?"

Kasa amsawa nayi saboda yanayin da na

shiga. Haka nan ko gaishe shi na kasa yi.

"Nasan kin yi mamakin ganina ba kuma

komai yasa nayi hakan ba sai dai don ganin da

nayi miki na cikakkiyar ya mai tarbiyya.

Wacce nasana kowanne yana y1 zata

zamanto mai bin umurnin iyayenta.

Ban tuntube ki na nemi ra'ayinki ba duk

kuwa da cewa idan na bukaci hakan mai sauki

ne a wurina, to sai na guji wasu abubuwa da ka

iya biyo baya. Ina fata za ki gafarce ni.

55

Ganin ban ce mishi komai ba, ba ni kuma da

niyya, sai kawai ya ci gaba.

"Ina da mata da 'ya'ya hudu, mata biyu

maza biyu. Ina kuma fata zamu samu fahimtar

juna ba tare da wata matsala ba?

Zan ba ki dan lokaci domin kiyi shawara,

don haka zan dawo a cikin sati mai kamawa."

Na ce, "A'a ba ma sai nayi shawara ba."

Ya gyara tsayuwarshi ya ce, "To menene

ra'ayinki?"

Na ce, "A gaskiya ni bani da niyyar yin aure

a yanzu saboda karatu nake, duk kuma abinda

zai shiga tsakanina da karatuna bana sonshi."

Ya dan yi murmushi kadan ya ce, "A'a ke

dai idan kina da wata matsalar kawai ki fadi,

amma ba wannan ba don kuwa ni kema kin san

ba zan hana ki karatu ba.

A matsayin da nake na Malaminki, kuma

nutsuwarki da na gani yasa nay1 takakka na

biyo ki.

To kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login