Showing 15001 words to 18000 words out of 23627 words

Chapter 6 - MAI DAKI (4) Book Complete By Hafsat C Sodangi.docx

22 Jan 2026

29

/>
Tana kukanta ina rike da cokali a hannuna

na kasa komai saboda takaici, shi kuma salad

dinshi yake sha tamfar ba a yi wani abu ba.

Ya kalle ni idan ba za ki iya zuba mun

abincin ba ajiye ki bani wuri. Inda zan iya da

ajiyewa nayi na tashi, to amma ba zan iya ba.

Na zuba mishi na kammala mishi komai na

mike na tafi dakina na zauna a bakin gado.

Maganganun Amina suna dawo min ban

taba jin mutumin da yayi mun irin wannan

zagin ba.

Kala Mallam bai ce mata ba saboda bani da

mutuncin da zata zage ni ayi mata magana.

Washegari kicin na fara shiga na hada abin

karyawa na dauka zan shiga naji su suna

magana.

91

Da alama kuma ba ta dadi ba ce, na karasa

dakin na zauna a kasa na gaishe shi ya amsa a

dake.

Na hada mishi nashi na mika mishi ya zuba

mun ido, nayi gaggawar sunkuyar da kaina.

"Gargadi na karshe da zan yi miki shi ne, na

kada ki sake zuba mun abinci ki tashi ki bar ni

da shi a wurin, shashashar yarinya kawai."

Na ajiye a gefe na tashi na shiga cikin bed

room din shi don na gyara, sai dai raina a

matukar bace.

Na gana abinda zan yi na fito na same shi

yana ee mata ba za ta yi ba. Idan kinga za ki yi

girkin da zaku ci da rana shi kenan.

Idan kuma kin ga za ki iya tilasta ni sa ta yi

miki girkin da zaku ci don kawai tana amsa

sunan matata sai mu gani.

Tunda na fahimci ba kya jin maganata. Na

gama shirina na fito muka tafi.

Makaranta kowa a shirye yake don fara

jarrabawa, kuma mun fito lafiya ba tare da

matsala ba.

92

Na biyo office din Mallam ba shi da alama

zai tafi yanzu, na ce ko zan tafi ne saboda mun

gama jarrabawa.

Bai kalle ni ba nima ban kara cewa komai

ba. Ba mu dawo ba sai wajen karfe uku.

Amina bata yi girki ba na shiga dakina ina

kokarin neman abinda zan ci saboda wata irin

gigitacciyar yunwa da ta kama ni.

Shayi na hada na sha wanda take kuma ya

burge mun ciki, nayi ta kwara amai babu

kakkautawa.

Nayi wanka na saka jallabiya na shigo cikin

jikina a mace na dauko indomie na yara na

dora a wuta cikin sauri ta nuna na ci na dan ji

dadi.

Sannan na koma nayi La'asar kafin na dawo

na dora abincin dare.

Duk abinda nayi kokartawa kawai nake yi

saboda wani zazzabi da ya rufe ni. Na hada

komai na kai mishi yadda muka saba.

Na zuba mishi abinci har yaci ya gama

Amina bata zo ba, ya kalle ni.

93

"Ke ba za ki ci ba ne?" Na ce, Bana jin dadi

ne. ya ce "Allah ya sauwake, amma da kin

daure kin ci ko babu yawa."

Ban yarda na ci ba don kuwa zuciyata ba a

nutse take ba.

Wajen karfe dayan dare na tashi saboda

murdawan da cikina ya ke yi, na shiga bayan

gida wani aman ne ya sake kubuce mun, nayi

ta yi.

Motsin da naji a bayana baisa na juya ba,

don na san Mallam ne. na wanke jikina na

dawo daki na kwanta.

Ban wani jima ba na sake komawa. Tun ina

aman abubuwan da na ci da rana har sai da na

koma kakarin aman kawai nake yi.

Amma babu abinda ke fita. Nayi matukar

galabaita.

Wajen karfe hudu saura kwata, Mallam ya

dauke ni zuwa asibiti, tun kan mu isa naji ni a

jike, abinda na dauka fitsari nake yi saboda

wahalar da nayi.

Sai dai ina fitowa daga cikin motar hasken

fitilun dake harabar wurin suka haskake mana

jinin da ya wanke illahirin kayan jikina.

94

Cikin wani irin firgita nayi luuu zan yi kasa,

yayi saurin rike ni. Daukata yayi ya shigar dani

asibitin take kuma Nurses da Likita suka yo

kaina.

Gwajin farko aka tabbatar mana ciki ne,

kuma ya fita. Wankin ciki aka shigar dani, shi

kuma ya juya ya tafi, don fara kiran sallar

Asubah.

Sun so su rike ni amma naki yarda, don

haka muka dawo gida wajen karfe goma.

Jarrabawar ranar dai ta wuce ni. Abin da na

ce wa Mallam kenans ai dai bai ce mun komai

ba, tukinshi kawai yake yi.

Muna dawowa gida kuma ya sake shiryawa

ya fita don zuwa wurin aiki. Labarin da Nasiba

taji ne yasa ta zuwa bayan gama jarrabawarta.

Ta zuba mun ido cikin mamaki.

"Kinga yadda ki ka zabge kuwa yau kawai?

Gaskiya kin ji jiki Hauwa'u, sannu."

Ina kwance na amsa. Sai lokacin ne Amina

ta shigo a'a kun zo ne? Nasiba ta fara gaisheta.

Suka gama gaisawa sannan tayi mun sannu

da jiki ta fita. Sai da Mallam ya dawo Nasiba ta

tafi.

95

Har cikin dakina ya shigo ina kwance a kan

gado na saboda rashin karfin da nake dashi.

Na dan yunkura na żauna ya ce, Yaya jikin

naki. Na ce da sauki. Ba ki da matsala?ie

Na ce, Eh sai ta rashin karfi, ya ce eh ai sai

a hankali wannan kuma. Don kin zubar da jini

da yawa, ga kuma aman da ki ka kwana kina

yi.

Na dan daga tafin hannuna ina kallo, shima

ya rike yana dan latsawa.

To amma Hauwa'u me yasa kina da ciki

har kin shiga wata na uku ba ki taba gaya mun

ba? Me ki ke nufi da hakan da ki ka yi?"

Yanayin tambayar tashi tayi mun wani iri.

Na ce, "Ban san ina da shi ba. Abin da na sani

kawai shi ne, na kan tashi da zazzabi da safe,

amma baya ga haka bana jin komai.

Sai aman da nayi jiya, shi kenan. Ya ce, To

Allah ya baki lafiya, na ce amin. Muka canza

maganar zuwa can kuma sai ya sake cewa, Ina

fata kin san da cewa maganar karatun ki ba zai

shafi al'amarin aurena da ke ba ko?

Na dan kalle shi zuwa can na ce, kana

zargin wani abu ne? yayi shiru na dakiku kafin

96

ya ce, a'a bana yi. Na ce to nayi maka

alkawarin ba za ka taba ganin wani abinda

baka so ba game da maganar karatuna ba.

Yace, To na gode, yayi mun sai da safe

sannan ya fita.

Duk da rashin karfina na lallaba naje

makaranta a washegari don jarrabawata. Shima

kuma yana jirana a waje lokacin jarrabawar ina

gamawa ya dauko ni ya dawo da ni gida.

Bai ce sai ya gama ayyukanshi ba. Duk

abinda nake yi daurewa kawai nake yi saboda

yadda zuciyata take cunkushe.

Babu abinda ya tsaya mun irin ganewan da

nayi har yanzu ban rabu da matsalar mahaifar

da na samu a gidan Ahmad ba.

Yanzu me zan yi a kai? Zan sami Mallam

nayi mishi bayani ne ko kuwa yaya?

Yamma tayi, ban yi kasala ba saboda

tunane-tunanen da ke damuna gara nayi aikin

da ke gabana kawai duk da rashin karfin jikina.

Na shiga kicin saboda na dora abincin dare

na samu Amina a ciki tana yi don haka na

dawo dakina na sake kwanciya.

97

Don haka a kwanaki biyunnan in banda

jarrabawata bana leka ko ina, ko wurin cin

abinci bana zuwa.

Shi ne dai yake shigowa ya dan yi mun hira

ya tafi saboda tunanin da yake yi na rashin

karfin jiki ke damuna.

Duk da jarrabawata ban ji kunyar shirya

lafiyayyen abinci ba, ranar da kwanana ya

zago

Nayi kwalliya mai ban sha'awa cikin yadin

material baki da pink mai rawa dinkin doguwar

riga ya kuma bi jikina ya manne saboda yaukin

yadin.

Ni kaina nasan ya matukar yi mun kyau,

don ya karawa hasken fatata kyalli. Na feshe

jikina da turare.

Sai da nayi sallah sannan na shiga falon.

A yanzu Amina ta daina yi mun shisshigin

makalkale Mallam ranar girkina, don haka ko

bana wuci sai nazo nake yi mishi abubuwan da

yake bukata.

Na shiga falon yana ganina ya dan saki

murmushin da ban san ko na meye ba a cikin

biyu, na ganin jikina yayi kwari ne ko kuma na

98

mai yaba kwalliyar dayar mu ba ne a gaban mu

ko zai yaba miki kwalliya to sai kun kebe don

gudun cin fuska.

Na karasa gaban shi ina zuba mishi abinci

na gama na zuba mishi abin sha na gyara zan

zauna ya ce ke fa?

Kamar nayi magana sai na fasa na dauki

plate ina zubawa Amina ta ce ai da ka barta

kawai kila bata jin ci ne. ka san illar bari yawa

ne da ita ballantana wanda a ka jawo shi da

karfi.

Ai ma an auna arziki da abin ya tsaya a

haka, ga yar makwabtan nan namu da suka

shigo duba ki shekaranjiya ai garin haka ita har

yanzu bata sake haihuwa ba.

Don an ce mahaifarta ta samu matsala

kawai fa akan tana Jami'a itama kamar dai

nakin nan."

Na kalli inda Mallam ke zaune yana cin

abinci sai dai fuskarshi ta canza gaba daya, na

zuba abincin na ja gabana zan fara ci.

Ta fara kokarin ci gaba da zanceen nace,

Amina ya isa haka. Ta kalle ni ta ce, au, ya isa

kuma kada nayi miki nasiha don na taimake ki?

99

Al ni 'yar uwa na dauke ki don kuwa ni ko

kishi da ke bana yi. Mallam ya ce, ta dai ce ya

isa haka ina ganin da sai kiyi shiru.

To ai shi kenan tunda dai duk bakwa son

zancen. Ita gaskiya kasan daci ne da ita

darling, amma tunda ba ka so shikenan.

Ta dan yi murmushi ta kalle shi, darling sai

da safe. Ina rike da cokali da abinci a plate ina

dan coccokalawa amma na kasa ci saboda

bacin rai.

Bana shiga harkar Amina, amma ita sai ta

shiga tawa. Har ya gama cin abincin bai sake

cewa komai ba.

Na kuma san dama tayi mishi maganar ne

don ta saka mishi damuwa a ranshi da zargi

wanda dama daga tambayar da yayi mun a

ranar da abin ya faru.

Ganin da nayi hankalinshi yana wani wuri

yasa na tattara abin da zan tattara na wuce shi

naje na kwanta.

Washegarin da muka gama jarrabawa a gida

na wuni. Ina zaune a gaban Baba Ladi don har

yanzu tana nan bata tafi ba, tana yaba mun

kyan da nayi.

100

Ta ce, "Gashi ba zama ki ke yi ba amma

kwanciyar hankali sai dai ina ga ko za a karbar

miki magani ne 'yar nan?

Na ce, A'a Baba Ladi lafiya kalau, ni kuwa

na fada mata haka ne don na san matsalata ya

kuma zamar mun dole na fuskanci Mallam

nayi mishi bayani.

Sai dai ta yaya? Tunanin da nake tayi

kenan. Ban koma ba sai da na jira dawowar

Babana nayi musu sallama bayan nayi musu

alherin da na riko musu.

A yanzu zamanmu da Amina ya canza.

Kasancewar mun gama jarrabawa ni ke yin

abincina na cikakken kwanaki biyu rana da

dare.

Babu damar na fito tsakar gida zan yi wani

abu ko zan shiga kicin sai ta fara zazzaga "

maganganun habaici iri-iri.

Ni kuma ban iya irin wadannan habaice-

habaicen ba, don haka bana kulata. Abinda na

sani shi ne, bata fito baro-6aro ta ce dani take

yi ba.

Duk da nasan dani din take yi, ni kuma bana

Son rikici.

101

Rannan na kwana dakin Mallam na fito da

sasafe cikin kwalliya sosai don yin abin

karyawa. Kamar yadda muke hutu suma

Malam Jami'a hutu suke yi.

Don haka shima Mallam baya zuwa aiki

kullum, sai ya dauro. Kokarinshi na ganin ya

kammala karatun shi ne na Phd din da yake yi.

Hakan ne yasa na kuke nake shirya mishi

gara iri-iri. Na shiga kicin na fara harhada

abubuwan da zan yi amfani da su, sai ga

Amina ta shigo.

Ta tsaya tana kare mun kallo, na ce mata ina

kwana? Sai da ta tabe baki sannan ta ce, lafiya.

Wai Allah ya rufawa mutane asiri kwashen

ragowar mutane darling ya dauko in banda

haka da ban san irin sanaben da aka yi mana a

cikin gidan nan ba.

Duk da 6ata mun ran da maganar tayi

kokari nayi na shanye amma sai na juyo na

fuskanceta.

Nayi murmushi na ce, Amina kenan, ai ni

ya kwaso ni yana da cikakken sanin cewa biyu

sun aure ni kafin shi.

102

Amma duk da haka ya aura yake kuma

ganin mutuncina da darajata da ta iyayena.

To amma ke fa? Matar da ya aura a zaton

budurwa ya ganta a burme ga kuma tsaraba a

Sunke jagwalgwalon 'yan birni?

Don haka duk abinda za ki gaya mun fade

shi ba zan ji haushi ba.

Na juya na ci gaba da aikina, kirjina sai

harbawa yake yi don naji zafin maganar da

Amina tayi mun.

Ni kuma nasan na fada mata ne kawai don

ramuwa ba wai don naji ba, asali ma ni ban san

komai game da ita ba.

Baya ga 'yan uwanta da nake gani suna

zuwa. Ban san lokacin da ta bar wurin ba, na

dai juyo ne ban ganta ba.

Na gama aikina na dauko a babban tray na

shiga falo zan ajiye na sameta a falon tana

zaune tana kukan sharbe shi kuma yana wasu

bayanai da ban fahimta ba.,

"Zo nan Hauwa'u". na dawo kan doguwar

kujerar da yake na zauna na ce gani.

"Me ya hada ki da Amina ki ka gaggaya

mata maganganun da kika yi mata na kalle ta

103

yadda ta dage take fyace majina da gefen rigar

barcin ta.

Na ce, Tazo ne ta ce maka na gaya mata

bakaken maganganu amma bata yi maka

bayanin dalilin da yasa na gaya mata ba?

Ke bana son surutu, ki bani amsar

tambayata kawai.

Nayi mishi bayanan komai da ya faru tun

shigarta kicin samuna da tayi da kuma maganar

da ta gaya mun.

Shiru yayi zuwa can ya ce ni na sanki

Amina nasan kuma ba karya tayi miki ba, kin

fada mata abinda ki ka fada wane hukunci ki

ke so nayi mata bayan ke ce ki ka fara gaya

mata bakar magana.

Duk lokacin da dayarku ta tsokani wata da

magana ta rama kada mutum ya zo wurina don

ya ji zafi.

Bana so, ya ya zan auro mata ki zo kina

gaya mata irin wadannan maganganun, idan

bazawara na auro ta ina ruwanki, ina abinda ya

shafe ki?

104

Ke na aurowa ita ballantana ki ce bata y

miki ba? Ai ni ki ka zaga ba ita ba. Ya kalle n

"Tashi ki hada mun abinci.

Na hada mishi abin karyawa na mika mishi

na hada mishi ruwan lipton a wani kofin na

ajiye mishi.

Bata nuna alamar ci ba don kuwa har yanzu

zaune take tana kuka tana fyace majina.

Ya gama karyawa na mike na dawo wurina

na kwanta doon na dan samu barci sai dai

hayani ya ce ta kaure tsakaninsu bana jin

abinda yake fada ita ce dai take bayanin ya

wulakantata.

Ya tona mata asiri a wajena, don haka ita ba

zata yarda ba.

Wasa gaske karamar magana sai ta zama

babba, kafin yamma ina kicin sai ga iyayen

Amina sun iso, Goggonta da kuma yar

Aminan

Na shiga dakin Aminan inda suke na gaishe

su, sannan na kai musu abin tabawa tunda ni ce

a kicin, na dawo na ci gaba da harkokina.

Ba a jinma ba aka yi kirana a falo na shiga,

gaba daya sun hallara. Na ce mishi, Ga ni

105

tunda shi ne ya kira ni ya ce yi musu bayanin

abinda ya faru dazu da safe.

Nayi bayanin komai suna salati suna

sallallami tare da tafa hannu, ita kuwa Amina

kuka take yi.

"Alhaji ka ci amanar son da yarinyar nan

tayi maka." Ya kalle ni "Tashi ki tafi." Na

mike zan tafi, Goggon Amina ta ce, "A'a ta tafi

ina, ai gara ta zauna ayi da ita tunda ko ta tafi

ma kawar da jiki ne kawai za a labarta mata

komai.

Tunda ta kai ma sirrin dake tsakaninka da

matarka dadadde ma bai tsira ba. Ya kalle ni,

ina ce ai ki ki ke yi? Na ce, eh. Ya ce To je ki

abinki

Na dawo kicin jikina a sanyaye magana na

gayawa Amina don taji zafin ta gashi ta zama

gagarumna.

To da alama dai kenan maganar da na fada

mata gaskiya ce ko kuwa yaya? Ba su fito ba

sai sallar Magariba.

Na kai musu abincin su dakin Amina, nima

na shiga dakina don gabatar da sallahta.

106

Mallam bai nuna min komai kan maganar

tunda da ni da shi ne kawai muka san

maganar bata taba shiga tsakaninmu ba.

Nayi ta ne kawail don na rama bakar

maganar da ta yi mun, ita kuwa Amina

tsakaninsu da darling din nata ya ki dadi.

Don ta kafe akan cewa ya wulakantata a

wurina, ya tona mata asiri. Zama tsakanina da

ita kuwa abin ba a cewa komai, don a yanzu ko

na gaisheta bata amsawa.

Idan kuwa a wurin cin abinci muka gamu,

to babu mai cewa wani komai. Ya hadamnu

yayi mana magana a kan hakan ta ce ita

tsakaninta da ni babu zaman lafiya har abada.

Idan ba kwatar mata hakkinta yayi ba. Za

kuma ta tabbatar na gane kurena. Ya ce to babu

laifi, ke Hauwa'u na ce na'am, ya ce ke ce

Rarama don haka kada ki gajiya. da gaisheta da

kike yi kullum.

Don Allah baya son gaba ta wuce kwana

uku, haka nan kada ki riketa da komai a cikin

ranki kin gane ko? Na ce eh ta kalle ni taja

tsaki ta tashi ta tafi.

107

Don haka bana jin haushinta, ya'yanta

kuwa 'ya'yan mijina ne, ina da kyakkyawar

alaka da su.

Koda basa zaman gida saboda makaranta,

don lokacin da su kenan mu'amallar da ke

tsakaninmu mai kyau ce.

A daidai wannan lokacin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login