Showing 9001 words to 12000 words out of 23627 words

Chapter 4 - MAI DAKI (4) Book Complete By Hafsat C Sodangi.docx

22 Jan 2026

22

kina ganin sai na hana ki ci gaba

da karatu bayan a halin da muke ciki zaki je aji

na uku ne."

56

Na kawar da kaina gefe na ce, Kawa

ra ayina kenan, kuma ina fata maganar zata

tsaya a nan."

Nayi mishi sallama na juya na shiga gida.

Na zauna a kan katifata cikin daurewar kai.

To ban kullaci Mallam Zakariyya ba kan

abubuwan da yayi mun ba don kuwa ma sai na

ce ban san abinda yayi mun mai tsanani ba.

Tunda bai fadar da ni ba kamar yadda nayi

zato ba daidai gwargwado, kuma abinda naci

shi ya bani haka nan rashin mu'amallar shi da

dalibai ba laifi ba ne.

Don kuwa yana kare mutuncin shi ne,

daliban Jami'a wasu ko ba ka neme su ba su za

su baka kansu, don shedananci.

Ko kuma don suci sakamako mai kyau. To

amma kwata-kwata ni bana ra' ayin shi.

Ban san dalili ba yanayin shi na dakewa

yana matukar fadar mun da gaba a duk sanda

na ganshi kuma sai na tuna da Ishak saboda

daurewar fuskarshi.

Mutane ne da basa murmushi sai da wani

dalili. Sannan kuma sai kawai a ganni a aji na

zama matar Mallam Zakariyya.

57

Kai abin zai yi mun wuya tunanina daya

kawai shi ne Babana ga dukkan alama kuma ya

yarda ya amince da shi.

Ga ni kuma abinda na gaya mishi a ranar tä

nuna yarda ne da maganar.

Idan kuma har zan sallami Mallam

Zakariyya to zan yi hakan ne cikin hikimar da

wani abu ba zai shiga tsakanina da Babana ba.

Shiryawa nayi tsaf cikin kasaitacciyar

kwalliya ta leshi coffee brown mai adon zare

sky bluc da pink na yafa gyaie pink na saka

takalmi na pink na rike purse pink na yiwa

Umma sallama.

Gidan su Nasiba na tafi.

Kasancewar ko kwana hudu bamu yi da

rabuwa ba, ya bata mamakin ganina.

Tana murmushi ke kuwa wannan irin

zukckiyar kwalliya kamar sabuwar amarya?"

Na ce, "To wa ya sani ne." Na labarta mata

komai da yake faruwa, tun daga kirana da

Babana yayi har zuwan Mallam Zakariyya da

abinda na gaya mishi.

58

Ta dan yi shiru zuwa can ta ce, "To amma

idan gaskiya zan gaya miki, to banga aibin

Mallam Zakariyya ba.

Mutum ne mai mutunci wanda babu wani

mutum da ya ta6a bada labarin mummunan

abinda yayi.

Sannann dan kankanin abinda yayi miki

kuma kema laifi ki ka yi mishi a matsayinshi

na Malami.

Kuma ko kina matarshi zai iya hukunta ki a

Makaranta don kuwa matsayinki na matarshi

daban matsayinshi na Malaminki daban.

Muna cikin wannan hirar ne aka yi sallama

da Nasiba. Ta kalli Usman yaron Yayanta da

yazo mata da sakon.

Ta tambaye shi wanda yake sallama da ita

ya ce ban tambaya ba, bari na koma ya dawo

ya ce wai in ji Malaminku ne Mallamn

Zakariyya.

Muka zubawa juna ido cikin mamaki ta ce,

"Lallai abin nayi ne. Bari na bude mishi dakin

baki."

Ta mike tsaye tana yafa gyalenta, na ce "To

kada dai ki ce mishi ina nan, yauwa.

59

Bata kulani ba wucewa tayi ta fita. Ni kuwa

tashi nayi na shiga wurin Hajiya na zauna

muna hirarmu, don kuwa mata ce ma

barkwanci.

Na kusa awa guda a zaune a dakin amma a

raina ina mamakin dadewan Nasiba, sai gata ta

shigo ta kalle ni.

"Dan zo mana baiwar Allah."

Na mike na bita a tunanin da nake yi ma ya

tafi, sai da muka fito ta co Kin gane ko, ina

ganin ya kamata ku dan fahimci juna, don ni

banga aibun shi ba.

Sannan ma mutunne mai saukin kai ba

yadda muke yi mishi gani ba a baya."

Dan mintina talatin dinnan da kuka yi shi

ne ki ka fahimci hakan?"

Ta ce, "A'a ba haka ba ne, amma to sai a ce

boye hali yayi ya biyo ta inda ya bi don neman

aurenki. Ke kin san kenan mutun ne mai

mutuncCi.

Don kuwa da da wata manufa yake nemanki

da ya dade da nunawa. Kada ki wulakanta shi

Idan kuma kin ga hakan bai yi miki ba shi

ke nan. Yana jiranki a falo."

60

Juyawa tayi ta bar ni a tsaye a wurin ta

shige dakinta. Na shiga falon da ta sauke

Mallam.

Ban samu daman daga ido na kalle shi ba,

saboda zuba mun idanu da yayi yana kallona.

Nabi kujerar da ke daf dani na zauna. Tun

kan na gaishe shi ya ce.

"Ina fata shishshige miki da nake yi ba ya

sawa kina kara tsanata?"

Nayi hanzarin dago kaina muka hada ido.

Ya ce, "Abinda na lura da shi kenan, bakya

ra'ayina.

To amma duk da haka ina so ki bani lokaci

da zamu fahimci juna a tsakaninmu. Idan har

na gane hakan ba mai yiwuwa ba ne.

To ina tabbatar miki duk yadda na matsu da

abin zan iya hakura.

Amma a yanzu idan k1 ka ki bani hadin

kanki to ba ki yi mun adalci ba. Bai kamata na

zauna ina gaya miki halin da nake ciki game da

ke ba.

Amma ina so k1 san abin. ya kai makura ne

yasa na kasa hakuri na kai ga yın magana.

61

A yanzu dinnan da nake yi miki maganar

nan shekaru bakwai ne da aurena da matata,

amma tun bayan nan ban sake kallon wata nayi

mata makamanciyar wannan magana da nake

yi miki ba a yau.

Ba ina yi miki maganar ba ne don kiji

tausayina ba, ni ba abin tausayi ba ne don zan

ya shanyewa na hadiye na bar shi a zuci1yata.

Tunda na dade ina shanyewa ba tare da

wani ya fahimci komai a kai ba, to amma ina

so na gamsar da zuciyata.

Na san nayi mata adalci ban hanata abinda

take so ba, sai bayan da na tabbatar yafi

karfina."

Ban cewa Mallam komai ba har yayi shiru.

Ya kalli agogon hannunshi ya ce, "Yanzu

karfe uku ne, 1ina ganin gara na hanzarta don

kada lokacin sallar La'asar ya riske ni a nan.

Zan samu alfarmar sauke ki a gida?

Na ce, "A a ba yanzu zan tafi ba."

Yasa hannu a aljihu ya ajiye kudi masu dan

auki a kan hannun kujerar da nake zaune a kai.

Ya ce, "Kiyi kudin mota don Allah a kula

yin dare ba shi da kyau."

62

Ban sake yi ma Nasiba maganar Mallam ba,

1ta ma bata yi mun ba.

Wata hirar kawai muka yi har ta rako ni na

shiga mota don dawowa gida.

Tsakanina da Mallam Zakariyyya kuwa

kullum yana kirana a da safe sai dare duka

kuma gaisuwa ce kawai sai ko dan maganar

karatu.

Ba a dade ba bayan nan muka koma

makaranta. Da farko dai naji nauyin abubuwa

musamman yadda zan fuskanci Mallam a aji.

Amma shima sai na gane ya basar, don haka

nima sai na shanye. Sai kawai na dauka babu

wanda yasan zance in banda Nasiba.

Bamu fi sati biyu da komawa makaranta ba

sai kawai kwatsam Babana ya saka daurin

aurena da Mallam, abinda yayi matukar dukan

zuciyata.

Na kasa sanin dalilin da yasa har yanzu

zuciyata ta kasa sakewa da lamarin shi,

mutumin da kowa yasan ba shi da wani aibu.

Haka nan ba ni da wani hujja na kin shi.

Wunin ranar ban iya tabuka komai ba.

63

Haka nan washegari ban tashi da niyyar

zuwa makaranta ba. Umma tana ta kallona har

ta gaji ta ce "Ni yau baku da makaranta ne

ko?

Na ce, " Muna da shi, bana dai jin dadi ne

kawai."

Waya yayi mun yana shaida min zuwanshi.

Na zurma hijabina na fita.

Kasancewar darc ne bayan sallar Isha'i a

zaune a motar shi na same shi.

Muna gaisawa ya fara tambayata dalilin da

yasa ban je makaranta ba.

Na ce haka kawai, da alama kuma amsar

bata yi mishi dadi ba. Saboda shirun da yayi na

dan wani lokaci kafin ya ce.

"Nasan anyi miki bayanin komai na game

da saka ranar aurenmu da aka yi, ina kuma fata

babu matsala ko?"

Nan ma shiru nayi ban ce komai ba, don ban

san abinda zan ce ba.

Idan ma da matsala wannan duk daga baya

ne don kuwa ba zai yiwu Babana ya zartar da

hukunci a kaina. Na nuna mishi cewa shi din

bai 1sa ba.

64

Lokacin da aka saka ba mai tsawo ba ne,

don haka ina so ki bani abubuwan da ki ke da

bukata da kuma shirye-shiryenki gaba daya.

ose Tunda ai kin san sati biyu ne ko? Na ce, ""Ni

bani da wasu shirye-shirye duk abinda aka yi

kawai ya wadatar ya ce, "To babu laifi.seo

nsm Kusan duk shirye-shiryen da ake yi na auren

Nasiba ce mai yi wanda ya dangance ni sauran

shirye-shiryen gida kuwa duk su Umma ne

suke yi.

Da alama kuma da gaske suke yi. Har kudin

bayan lefe Nasiba ya baiwa ta narko siyayya ba

na wasa ba.

Ganin irin hidimar kashe kudin da yake yi

yasa na rubuta mishi tevt a gajarce.

"Ina fata ka san nayi aure biyu a baya?"

A take kuma ya turo min da amsa.

"Na sani akwai matsala ne? "

Don haka sai kawai na rabu da shi.b ionids

A makaranta kuwa satin da maganar ta bazu

sai da naji kamar kada na sake zuwa.

65

Kowa maganar yake yi rakwacam babu tsari

wasu ma cewa suke yi dama shi ne ya daure

mun gindin cin jarrabawar da nake yi.

Duk inda na zauna kuma idan mutum yazo

mace ko namiji sai ka ji ya ce amarya

Congratulations muna taya ki murna fa wani

idan ya tsaya a nan wani sai ya kara don neman

bugun cikin yayinda wasu kuwa gaskiyarsu

suke fada taya ni murna suke yi.

Shi kuwa duk yadda yayi da ni na gaisa da

abokanshi naki yarda.

Don kuwa nasan abokan nashi ba za su

wuce Malamanmu ba.

Idan da don tani ne da ko 'yar walima ba ayi

ba, to amma Nasiba ta ki.

Gayyata sosai tayi, yan makarantarmu

kuwa sun amsa gayyata, ga kuma taron dangi

da abokan arziki. Amma komai na dangin

abinci da na sha sai da ya ragu.

Ana daura aure kuwa a washegari aka kai ni

gidan Mallam. Har a wannan lokacin kuwa da

aka watse a ka barni daga ni sai Nasiba,

Zuciyata a kuntace take.

66

"Da kin yi hakuri kin saki ranki ni fa nafi

zaton tsoro ne ya hana ki zuciyarki ta sake.

Kuma gaskiya ne a tsoracen nake don kuwa

ban san bayan auren me zai biyo baya ba, haka

nan shi wannan auren shi ne na karshe ko

kuwa shima matsala zata taso ne a sake sakina?Bayan na fara sakewa na mayar da gidan

gidan zamana? Idan da a yadda naso ne to da

zan dau lokaci ban yi wani auren ba.

Don kuwa babu abinda naki irin a zauna

zaman kirga mun aure.

Nasiba bata tafi ba sai da Mallam ya shigo

bayan an idar da sallar Isha'i.

Da kanshi kuma ya mayar da ita gida bayan

yayi mata godiya.

Duk yadda nayi zaton abin zai zamo sai

naga ba haka ba, don kuwa cikin kankanin

lokaci sai Mallam ya sauya mun tunanina.

Don kuwa sai na gane shi mutum ne mai

wani irin rarrashi da saukin kai.

Da sassafe na tashi na dan yi abubuwan da

zan yi irin su wanka, na kuma kintsa kaina

cikin yadin shadda gizna, doguwar riga mai

laushi.

67

Nasa gyale mahadin ta na rufe jikina. A falo

na zauna ina karewa falon kallo.

Yayi kyau ba kadan ba, ba wai tsadar kayan

ba sai dai kyan tsarin da aka yi mishi ne zai

baiwa mutum sha'awa.

Komai na cikin shi kore ne mai haske.

Kama daga kan labule, kujeru, centre rug har

door mat dan sirkin ba mai yawa ba ne.

Ban dade da zama a wurin ba Mallam ya

shigo. Sanye da jallabiya fara sol a jikinshi.

Kusa dani yazo ya zauna a kan doguwar

kujerar da nake.

Na dan takura kadan saboda yanayin zaman

da muka yi. Ya ce, "Amarya an tashi lafiya?

Na fara gaishe shi yana amsawa ya ce,

"Kiyi hakuri kin tashi ba ki ganni ba na tsaya

ne a masallaci meeting na committee kan wasu

yan abubuwa da ke tasowa a unguwa.

Ina fata babu matsala dai ko? A hankali na

ce "Eh." Ya ce, "To an gode, Allah za ki zo

wurina ne mu karya gaba daya ko?"

Na ce, To. Yana gaba na bishi a baya zuwwa

inda ya kira sashenshi.

68

Tankamemen falo ne kawatacce da kujeru

masu kyau sai tibi na bango babba, sosai na

zauna akan daya daga cikin kujerun, shi kuma

ya shiga wata kofa ya dan dade kafin ya fito.

Fitowarshi babu dadewa wata mace ta shigo

doguwa ba sosai ba, yar siririya wankan

tarwada, don kuwa na fita haske sosai

Sai dai kyakkyawa ce sosai. Sannan 'yar

gaye a kallon da nayi mata da bai fi na dakiku

biyu ba.

"Sannu Hauwa'u an tashi lafiya?"

Ba sai wani ya tsaya yi mun bayanin komai

ba, take na fahimta amma duk da hakan sai

Mallam ya ce.

"Hauwa'u ga Amina nan 'yar uwarki ce."

Ta karasa kusa da shi ta dan zauna a gefe

tana mishi magana da ban san me take fada ba.

Na ji ya ce, "A abana so. Ta waiwayo ta

kalle ni.

"Ina kwana Hauwa'u, an tashi lafiya ko?"

Sannan ta sake fita sai gata da manyan kula

guda biyu take kuma ta fara zuba abinci tana

ajiyewa. Sai da ta gama zubawa sannan ta ce

nazo muci.

69

Muna zaune muna ci kowa dai da nashi, sai

dai na kasa sakewa ko kadan babu abinda nake

So kin na koma dakina su kuwa suna ta dan

hirar su.

Ya kalle ni "Yaya dai Hauwa'u, akwai

matsala ne?"

Na ce, "A'a babu." Amina ta ce, "Kila

kunyata take ji ko don dai nasan wannan

kunyar ba ta daling ba ce. Tunda ba yau aka

fara ganin juna ba."

Ni kuwa wani irin abu nake ji a zuciyata ba

6acin rai ba, haka nan ba haushi ba.

Amina ta gama cin abincinta ta mike ta fita

ta bar ni rike da plate a hannu.

"Kokarta kici abincin nan ko babu yawa.

Abinda ya fara fada mun kenan, bayan fitarta.

"Ko kuma kin fi so na ba ki da hannuna'?

Na dago ido zan kalle shi, na kasa saboda

kallon da yake yi mun. ban iya ci ba don haka

na hakura na ajiye.

Ya mike ya isa gaban fridge din dakin ya

dauko robar fresh milk da dogon kofi yazo

kusa da ni a kasa ya zauna ya tsiyaya ya dauka

ya nufi bakina zai ba ni da kanshi.

70

Na girgiza kai na karba da hannuna bai hana

ni ba sai kawai ya sake mun ya ce, "To amma

fa ki shanye duka kafin na dawo daga dauko

yara daga Islamiyya.

Kin san yau Lahadi da safe ake zuwa." Na

ce, To. Ina so na koma dakina. Ya ce, "A'a ki

zauna a nan idan kuma barci ki ke ji ga daki

nan ki shiga.

Bai fi mintina talatin ba da fita sai gashi ya

shigo, yara guda uku suna binshi a baya mza

biyu da karamarsu mace.

Dukkansu suna ba shi labarin abubuwa yazo

ya zauna ya ce, "To ba ku gaisa da Mamanku

ba?"

Gaba dayansu suka fara gaishe ni a tare

cikin fara'ata nima na amsa. Karamar ta ce,

"Baba ita ce sabuwar Mama ko?"

Ya ce, "Itama Ummulkhairi ashe kin gane ta

kenan? ta kada kanta alamar eh, ya ce "To

kuje ku huta ku cire kayan makaranta ku ci

abinci."

Suka ce, "A'a Baba mu a nan zamu ci. Ya

bude musu ido ya ce, "Kai ku tafi ku bani wuri

na ce."

71

Karamar tasa kuka, ta juya tabi yan uwanta

suka fita

Ina ganin ya kamata ki kwanta ko ban ce

mishi komai ba don kuwa ba zan iya musu da

shi ba.

Kwanana biyar a gidan Nasiba ta dawo. Na

harareta lokacin da naga shigowarta, na ce

Don wulakanci yau ne ki ka ga daman zuwa?

Ta ce, "A to ban yi kokari ba kenan, ai da

cewa nayi sai kin yi sati biyu."

Na ce, "To ai sai ki koma. Ta isa gaban

fridge din dakin ta ciro lemon kwali ta zauna

tana surkawa da ruwan sanyi saboda bata son

zaki sosai.

Amina tayi sallama. Gaba daya muka amsa

sallamar, ta nemi wuri ta zauna suka fara

gaisawa da Nasiba.

Sannan aka shiga hira gaba daya. Ta kai

mintina goma sannan ta tashi ta fita.

Nasiba ta ce da alama dai matar nan za ayi

zaman kalau da ita? Na dan yi murmushi muka

shiga wata hirar tana tambaya ta ranar da zan

koma makaranta.

72

Na ce, "Na jira ne naji ya ce mun mu tafi to

har yanzu bai ce ba."

Nasiba ta ce, "Kenan za ki jira ne sai ya ce

ki tafi, ina ce kwanaki uku yayi a dakin nan ya

fita?

Na ce, Eh mana, to da nawa ki ke so yayi?

Ta ce, "A'a ba wannan ba ne ma, ki dai sani

ne cewa ya kamata idan ku ka zauna kiyi mishi

maganar komawarki makaranta.

Kasancewar yau kwanakina biyar ne a gidan

to kuma a dakina Mallam yake.

Don haka kokarina shi ne na ganin nayi

mishi maganar Makaranta na tunda na kusa

kwanaki goma ban je ba.

Don tun kafin daurin aurenmu na daina

zuwa. Muna zaune a falo dukkanmu hira ake yi

tunda a can muke cin abincin dare gaba

dayanmu.

Sai dai ni kam duk hirar da suke yi ban iya

tsoma musu baki, idan ba saka ni a ciki aka yi

ba.

Hankalina a zahiri yana kan shirin da ake yi

ne a TV sai dai a badini ba haka ba ne.

73

Ban saba ganin mace tana yiwa namiji

abubuwa haka a gabana ba. Na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login