Showing 36001 words to 39000 words out of 56966 words
Chapter 13 - WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf
samu Laila ta bayyana mishi tarihin rayuwarta da ta
voye ko zancen, ba ta so.
Domin a ganinta ta riga ta tsere, ta yi nisa da rayuwarta ta baya. Wannan karon ma suka hau
jirgin kasa ta hanyar amfani da ‘oyster’ dinsu. Rataye da ‘picnic bags’ dinsu. Mai dauke da
abinda zasu ci, da wanda zasu sha, ‘camera’ da sauran su.
Lailah sanye take da bakar ‘coat’ wadda ta zo har gwiwoyinta da bakin wandon ‘channel’. Ta
yane fuskarta da kankanin gyale daga ‘pashmina’. Ta saje tsaf da turawan Ingila, ta yadda in ba
fada maka aka yi ba ba za ka iya tsince ta daga cikin su ba.
Yayin da Abbas ke sanye da shudiyar suwaita long sleeve da bakin ‘jeans’ shima, kai da
ganinsu ka ga ‘students’ zaunannun Birnin Sarauniya.
Zaune suke a bakin ‘Lake’ din kafafunsu duka cikin ruwan. Abbas ya dube ta da kammalalliyar
fuska, ta samu kanta da jin wannan mutum kamar Yayanta Isma’il, zuciyarta ta amince da shi.
Ita kanta bata san dalili ba.
Ya ce, “Lailah is high time in ji abin da ya rabo ki da gida, ko zancen wani da ya shafe ki baki
tava yi min ba. Jikina ya bani ba haka kawai cikin dadin rai kika zo karatu kasar nan ba. Is this
friendship?”
Ta ce, “Zan gaya maka Abbas, duk da cewa ban san karvar da za ka yi wa labarin ba”.
****
FARKON LABARIN
Haduwata da Mohammed, a babban filin jirgin saman Egypt ne (Cairo International Air-port),
za mu raka mahaifinmu zai tashi zuwa kasar Najeriya. Mahaifinmu dan uslin kasar Najeriya ne,
dan Kano, amma mazaunin Egypt, tun daga zuwa karatu ya samu aiki saboda kyawun
takardunsa. Likita ne kwararre a ‘general hospital’. Ya yin da mahaifiyarmu ta kasance ‘yar
usulin kasar Egypt. Ya aure ta tun auren saurayi da budurwa.
‘Patient’ dinsa ce tana da ‘ulcer’, ya kasance duk wani ‘treatment’ dinta a hannunsa yake.
Suka gina ma zuciyoyinsu wata irin soyayya wadda daga iyayenta basu samu wata matsala ba,
wai don kasancewar shi ba dan kasa ba.
Shi daman maraya ne ba uwa ba uba. Sai Baffanninshi biyu a Kano. Suka yi aurensu a nan
Egypt ya sayi babban gida a can suke zaune cikin soyayya da amana.
Isma’il shine babban dansu, sai ni, sai ‘yan biyun Momi Sanah da Najat. Mohammed matukin
jirgin sama ne, wannan shine babbar matsalar da muka fara cin karo da ita a rayuwar aurenmu.
Shi Mohammed dan asalin garin Bauchi ne, wani gari Jama’are. Su biyu kacal iyayensu suka
haifa daga shi sai kanin shi Sa’eed.
Akwai rata sosai ta shekaru goma tsakanin Mohammed da Sa’idu. A lokacin da aka haifi Sa’id,
girma sosai ya cimma mahaifinsu Malam Yahya, wannan ne dalilin da ya sa Sa’eed ya dawo
hannun mu da zama lokacin yana karatu a Tafawa Valewa University Bauchi.
Mohammed ya ware ma Sa’eed dakin zama a boys kuaters, ya fara karatunsa cikin nasara.
Inda yake karantar ‘Geography’. Wankan tarwada ne mai kyakkyawar sura, yana da
kazar-kazar da fara’a mai yawa, yana da kirki da ladabi ga dan uwansa, da ni da nake matsayin
matar Yayansa. Kirkin Sa’id ne ya sa muka zamo wasu irin aminai, duk abin da ke damuna kafin Mohd ya sani
na fadawa Sa’id.
A ganina shine mai lokacina, saboda mijin bana jin dadin sa. Mohammed, wani irin mutum ne
tough, serious, ba shi da lokacin iyalinsa ayyukanshi na tuki suna gaba da komai.
Sai ya yi watanni uku yana yawo a duniya. Da fari na uzurce shi da cewa yanayin aiki ne, amma
a matsayina na mace mai jini a jika wannan aikin na Mohd. na ci min tuwo a kwarya.
Farkon auren mu ya zamanto ba haka bane, don a lokacin yana fafutukar neman aiki ne muka
gamu. Da ya samu aikin ne abubuwa suka sauya, don haka zuwan Sa’id gidan mu ba karamin
farin ciki hakan ya haifar min ba.
Digirina na farko na yi shi ne daga jami’ar Al-Azhar a kan Falsafa (Philosophy). Ina matukar son
mijina kwatankwacin yadda yake so na. Domin a kan soyayya da kauna muka gina auren, tun
mahaifina yana raye. Mohammed ya dauki son duniya ya dora a kaina, sai dai kuma abin
takaicin ba shi da lokacin da kowacce mace take bukata tare da maigidanta, yana hadawa
kanshi zafi da yawa kamar shi kadai ne matukin jirgi a duniya.
Daga baya ne Sa’id ke yi min bayanin ai bayan Virgin Atlantic da yake wa aiki wasu kamfunan
daga ko’ina irin su MEA, KLM, Royal Air Moroc, da sauransu suna daukar shi haya saboda
kwarewar sa.
Amma a matsayina na matarshi abokiyar rayuwarshi bashi da lokacin da zai zauna ya yi min
wannan bayanin, sai dai kullum ya ce bana yi mishi uzuri da yawan ayyukan da ke gabansa.
Sa’eed ya dawo makaranta a wani yammacin Litinin ya same ni a kitchen, yai sallama ya shigo,
ya karve ni a firar dankalin da nake yi.
Ya ce, “Gaskiya Aunty Lailah ya kamata a samo miki yarinya mai aiki mace kina wahala fa, ke
kadai a gidan nan”.
Na ce, “Da hakan za ta faru da na yi murna”.
Ya ce, “On weekend, (cikin karshen sati) zan je Jama’are zan fadawa Hajiya za a samu insha
Allah”.
Na ce, “Na gode”.
“Yaya bai yo waya ba? Ina so in mishi zancen kudin ‘registration’ ne. Kin san an ce shekarar
kwana gashi har shekara ta zagayo za mu shiga level 300”.
Na ce, “Har nawa ne?”
Ya ce, “Bai kai 20 thousand ba”.
Don haka a daren ranar na kirgo kudin registration na ba shi cikin kudin da Mohammed ke bar
min.
Ban rasa ci ba, ban rasa sha ba, ban rasa suttura ba, amma na rasa soyayya da kulawar mijina.
Sai Sa’id ya zamo wani mutum mai kula da ni da debe min kewa, ta hanyar irin wasannin nan
na kanin miji da barkwanci ga matar Yaya.
Shakuwar mu da Sa’eed din har ta zarta misali, saboda yadda yake nuna min kulawarshi a kan
al’amura na da damuwarshi a kaina.
Idan ka ganmu a kanti muna sayayya ko a kasuwar wunti muna cefane sai ka dauka mata da
miji ne.
A satin muka shirya tafiya Jama’are ni da Sa’eed gaida Hajiyar Mohd. Hajiya ta rasa inda za ta
sani don murna, ta kuma rike ni sai na kwanan mata biyu. Don ita kanta wannan yanayin aikin
na Mohd. na damun ta, don dai ba yadda za ta yi ne.
Da daddare mun yi shirin kwanciya Hajiya ke yi min nasiha cikin hikima na in kara hakuri da
yanayin aikin Mohd. Ita kanta ta damu, to amma yaya zamuyi? Tunda dai hanyar abincinshi
kenan, kowa da inda Allah Ya tsaga mishi hanyar abincinsa.
A raina na ce, “In ban yi hakurin ba ya ya zan yi? Ya riga ya rabani da uwata da ‘yan uwana,
kuma ba shi da lokacina.
Idan dai don kudi ake wannan aikin babu samar ma kai da zuciya, kwakwalwa hadi da gangar
jiki hutu, sai in ce ban san inda Mohammad zai kai kudin da yake samowa ba”.
A kan hanyarmu ta dawowa Sa’eed ya dukufa lallashina, don ko fuskata mutum ya kalla ya san
ina cikin matukar damuwa.
Yake ce min, “wata rana sai labari Aunty Lailah, ki kara hakuri a kan naki na da, shi Yaya da
kanshi zai gane wata rana ba ya kyautawa, ya ragewa kanshi aiki ya rungumi iyalinshi, in kuma
kin amince in yi mishi magana to, duk da yana daga cikin irin mutanen da da wuya ka doshe su
da irin hakan”. Ban ce komi ba, abin da na sani shine, auren Mohammed ya fice mini a rai, burina tunda ba shi
da lokacina, to ya sallame ni in koma cikin ‘yan uwana gaban mahaifiyata, duk da bai tava
iyakance min zuwa ganin su ba.
Shakuwar mu da Sa’eed sai abin ya kara gaba. Ya zamanto girki ma wannan tare muke yin sa,
kallon kwallon kafa da daddare duk tare muke yi, kamar wasu mata da miji.
Har na kan kissima a raina wani lokacin ni kam da ma Sa’eed aka aura min da na more. Duk da
yake yaro dan shekaru ashirin da bakwai ya sn yadda zai yi ya tafiyar da mace da nuna mata
abin da ta fi so a gidan aure, wato soyayya da kulawa.
Za ka so ganin mu muna kallon ball har da tafawa, saboda shi dan ‘Arsenal’ ne ni ‘yar ‘Real
Madrid’, mu takarkare mu yi ta musu kowa yana kare kungiyar sa.
Mu yi girke-girke mu ci, a karshen mako mu yi ‘sanitary’ mu gyare ko’ina na gidan mu.
Yana da yawan zama a ‘study’, musamman lokacin jarrabawa ba ya wasa. Yaro ne haziki mai
kirkin gaske da saurin shiga rai.
A satin da su Sa’eed suka fara zangon karatunsu na farko a level 300, Mohd ya iso, kai ka ce
ba mijina ba, ban yi wani doki ba balle in yi wasu shirye-shirye domin tarbarsa.
To shima din bai damu ba, don ya san shi din har kullum mai laifi ne a gare ni, bayan a ganin sa
yana sauke duk wasu nauyi da Allah ya dora masa a kaina idan ya zo bayan kowanne watanni
ukku.
Ya rage nawa in dubi yanayin aikinsa inyi mishi uzuri ko kar in yi, don shi kan ga yadda ya nuna
ya gaji da kananan korafe-korafen da nake damun shi dasu a kan rashin sa cikin gidan, tun da
dai ba dauka na zai yi ya goya ya dinga yawo dani cikin duniya ba. Bai kuma iyakance min
zuwa ga ‘yan uwana a duk sanda na so ba. To amma mene ne auren? Ina da tambaya, ‘yan uwana mata. Shin wannan shine ginshikin
auren ko me? Ba na samun ginshikin aure, don haka am not satisfied with my husband.
Don haka Mohammed har ya gama kwanakin shi biyu ya koma bai samu wani edcellent
welcome daga gare ni ba, kamar yadda shi ma ya ke complaining(korafin) na hana shi hutawa,
na dauki vacin ran banza da wofi na daurawa kaina.
Idan bai fita ya nemo min ba me zai ba ni? Ko nufina shine ya jive a gida kada ya yi amfani da
damar da Allah ya ba shi na morar iliminsa? Mutane nawa ne suke neman ‘chances’ din
(damar) da yake samu basu samu ba?”
“Su ‘chances’ ba a hakura da wasu don a huta, a kula da bukata da rayuwar iyali?” Na
tambayeshi watarana.
Ya ce,
“Lailah you’ll never understand me, (bazaki tava fahimtata ba), tunda kin riga kin damu kanki.
Na gane ki, irin matan nan ne da suke so miji ya like musu kamar kaska, kin san da irin aikina
kika aure ni, a kan me yanzu za ki uzzure ni?”
Don haka har ya koma bamu yi rabuwar arziki ba.
Ta duba agogon hannunta kana ta dubi Abbas.
“Ya kamata mu tafi gida haka yamma ta yi sosai”.
Abbas ya zare kafafunshi daga cikin ruwan suka mike suna harhada kayansu.
Ya ce, “Ni dai na so ki karasa min labarin nan a yau”.
Ta ce, “Some other tym, bana jin dadin jikina sosai, sannan ga yamma ta yi”.
Suka jero suna tafiya cikin hirarraki kanana, sai ka rantse mata da miji ne”.
****
Abbas ne a kitchen din gidan yana kiciniyar daura masu sanwar abinda za su ci da daddare. Ba
komi bane ‘source’ ce da za a ci da biredin alkama.
Ya kammala y rufe komi ya gangara kantunan dake kasa ya mika ‘yan sisinsa (penny) ya sayo
biredin ya dawo kitchen din, ya dauki na Lailah da nufin ya fara mika mata kafin ya dawo ya
dauki nashi.
Ya iso jikin kofarta ya kwankwasa, shiru ba a amsa ba. Ya sake kwakwasawa a karo na biyu......
A wannan lokacin da ya dan saurara, sai ya jiyo tana kakarin amai kamar fitar rai.
Don haka ba tare da wani tunani ba ya murda kofar a sukwane ya isa gefen gadon da ta jike da
amai, ya aje plates din da ke hannunsa a gefe.
Ya ce, “Lafiya Lailah?’
Cikin tsananin tashin hankali da firgici bayyananne, zane varo-varo a kyakkyawar fuskarsa.
Ta yi mai nuni da ya ba ta ruwa, ya dauko gorar ruwa a ‘bed-side fridge’ dinta ya valle hancin ya
mika mata, ta kuskure baki ta wanke fuska. Ta koma jikin filo ta kwanta tana maida numfashi a
galabaice.
Duk abin da ta saka ma cikinta a yinin ranar ta amayar da shi, har da wani kore-kore cikin
aman. Sabida babu sauran abinda za’a amayar din.
Ya zage tukuru yana gyara wajen bayan ya tattara zanin gado ya jefa a bokiti.
Sai da ya gama aikin aman tas ya fesawa dakin ‘room-fresh’ mai dadin kamshi, zuwa lokacin
Lailah ta fara rawar dari, hakoranta sun soma karo da junansu.
Ta ce, “Rufa min bargon nan, Abbas sanyi...”
Ya dauki lallausan bargon ya rufa mata, amma ba ta daina rawar darin ba sai ma abin da ya
karu.
Don haka ya gangara kasa ya koma nashi dakin ya dauko nashi bargon ya kara mata. Ya koma
kan kujera daya kwallin-kwal dake cikin dakin ya zauna cikin kulawa ya ce.
“Za ki iya kokartawa muje asibiti?”
Girgiza mishi kai ta yi alamar “A’a, ba za ta iya ba”.
Lallai lafiya… uwar jiki, lokaci daya ta rafke Lailah a daki, shima ta hana shi hidimomin gabansa,
balle halartar ‘lectures’.
Ya je dai ya ba da edcuse a kan Lailah, amma shi ba shi da hujjar da zai bayar. Don haka ciwon
Laila tsawon sati guda ya shafi karatun sa ba da wasa ba.
Wannan ba shine a gabansa ba, lafiyar kawarshi, abokiyarshi, aminiyarshi Lailah ne.
A rana ta bakwai ne dai ya takura mata ala dole ta mike, duk ta rame ta zaizaye dama jikin ba
wani jiki ba.
Ya dauko jibgegiyar coat dinta ya jibga mata, ya manna mata bakar hula da socks na hannu.
A wannan lokacin na karshen watan January, lokacin da London ke fama da snow , har ya
soma tunanin rashin sabo da yanayin ne ya haifar ma da Laila wannan mugun zazzavi da
vomiting. Wato (amai)
To amma ina ruwan sanyi da vomiting (amai)? Haka dai suka gangara kasa, suka hau bus, ko
da yake daga nan ma unguwar da suke (Acton Town) za su iya karasawa NHS da kafafunsu,
sai dai don baya so ta jigata ne.
Abinki da dalibai ma’abota inshora, nan da nan su kai ‘booking’ ganin doctor, aka soma daura
Lailah a kan gwaje-gwaje, wanda ya kai su hard a su dibar fitsari, jinni, don binciken zahirin abin
da ke dmaun ta.
“Congratulations!”.
Siririyar Baturiyar ta ce da shi tun kamin ta iso kujerar da suke zaune. A tsammaninta su din
mamallakan juna ne (ma’aurata).
Ta sake cewa, “Congratulations, nan da watanni bakwai muna maka albishir din mallakar
bouncing baby”.
Daga shi har Lailah ba su fahimce ta ba. Don haka ya kama hannun Laila kada ta fadi suka
koma ofishin doctor.
Ya ce, “Meke faruwa ne doctor? Me ke damun Lailah?”
Ya washe baki shi ma cikin yi mishi albishir din cewa matar shi na dauke da juna biyu ne”.
Wata kara da Lailah ta saki ta kuma sulale a nan ta fadi sumammiya ta razana su. Abinka da
wadanda suka san muhimmancin patient, nan da nan aka yi rubdugu a kan Lailah aka kuma
umarce shi da ya fita.
Ya dawo bakin kofar dakin likitan ya jingina da bango, hankalinsa ya masifar tashi, ya rasa
dalilin suman Lailah don anyi mata albishir din kasancewar ta mai juna biyu.
Ba da auren ta ba? Me zai dame ta don an ce tana da juna biyu? Duk da can a karkashin
zuciyarsa wani dunkulallen abu ne ya tokare kirjinshi, tun sanda Lailah ta soma ba shi labarin
rayuwarta, ya kuma fahimci tana da aure, ya soma canja tunanin shi a kanta, ya kuma yi dalilin
da ya sa ya fara ja baya da ita, amma tun da ta fara ciwon ya samu kanshi da son taimaka
mata.
Amma bai ga dalilin da don an ce tana da juna biyu za ta daga hankalinta ba. Al’amuran
rayuwarshi gaba daya sun canja, tun haduwar shi da Lailah.
Yana fama da wani lamari mai girma cikin zuciyarshi a kanta, shi kadai ya san halin da yake ciki
a kan Lailah, dare da rana, wuni da safiya. Tun a ranar da ya soma dora idanunshi a kanta.
Hatta a marigayiyar matarshi bai tava tsintar kanshi a al’amarin dake faruwa da shi a yanzu
game da Lailah ba.
Ba ya tantama soyayya ce mai girma, kuma mara adalci. Tun da dai wadda ake mawa matar
aure ce ga wanin sa. Don haka ya san cewa al’amarin ba zai tava yiwuwa ba.
Kwanansu biyu a asibitin ana yi ma Lailah karin ruwa da kulawa ta musamman. Tunda Lailah ta
dawo cikin hayyacinta kuka take, wanda bai san dalilin sa ba.
Rarrashin duniya Abbas da ‘nurses’ sun yi amma kamar kara izata suke, har aka sallamo su
suka dawo gidan da suke zaune Lailah ba ta bar tsiyayar da hawaye ba.
Ya yi sallama a kofar dakinta dauke da plate na soyayyar ayaba (plaintain) da apple (tuffah) a
cikin leda, da fresh milk har da ‘ya’yan inibi.
Ya ja tebir ya dora mata ya sanya ta a gaba a kan dole sai ta ci, ta soma ci kamar mai cin
magani, ta rasa inda za ta sa kanta. Rabonta da abinci har ta manta.
Kuka take wurjanjan a lokacin da take rokonsa da ya taimaka mata a cire cikin da ke jikinta.
Abbas ya sa mata ido yana kallon ta, a ladabce ya ce.
“Lailah”.
Ta saurara da kukan ta dube shi tana shessheka.
“Ke fa da bakin ki kika gaya min cewa kina da aure?”.
Ta daga mishi kai bayan ta sa havar kallabinta ta fyace wata matsiyaciyar majina.
“To ‘why’ (meyasa) za ki ce a kashe rai alhalin da ubansa?”
Maimakon ta ba shi amsa sai ta kara tsinkewa