Showing 12001 words to 15000 words out of 56966 words
Chapter 5 - WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf
nan gida Najeriya”.
Suka yi sallama kowannen su zuciyar kamar-kamar me.
A iyaka tunaninsa, bai san laifin da ya yi ma Lailah takamaimai ba, lafiya kalau suka rabu. Sai
dai da ya yi nazarin wasikarta ya fahimci a kan halayyar da yake mata ne ta gwammace ta yi
nisa da shi, tun da ta kasa magantawa kanta, shima ya kasa maganta mata.
To a yau ga shi a dalilin halayensa aikin ma gaba daya ya kasa a dalilin rashin ta.
Daman an ce baka sanin muhimmanci da amfanin mutum sai ranar da ya suvuce maka. Ya rasa
inda zai sa kansa a dalilin rashin Lailah, ya yi nadama matuka da irin halayen da yake yi mata
wanda ba sau daya ba, ba sau biyu ba ta sha gaya mishi cewa ba ta so, ya daina.
Amma bai dainan ba, sai sanda ya rasa ta. Shi da dan uwanshi suka shiga kafafen yada labarai
na garin Bauchi suka sa cigiyar Lailah har da hotunanta.
Amma har kwanaki suka tura shiru kamar an shuka dusa. To ina ga mahaifiyarta da ta tsugunna
ta haife abarta?
****
Ya kwankwasa kofar dakin a hankali rike da karamin ‘tray’ da ya dauro karamin ‘tea flask’ da
kayan shayi.
Ta zo ta bude cikin nutsuwa ta yi wani irin fari ta rame ta zuge duk a lokaci daya. Ya aza ‘tray’
din a kan wani dan karamin tebir da ke dakin, ya ja kujera ya zauna ya soma hada mata shayin,
ya kammala ya shiga firfitawa.
Kallon shi take cike da tausayin kulawa da taimakon da yake yi mata a matsayinshi na wani
mutum da basu hada dangantakar komi da shi ba, face abokin kan hanya kadai.
“Abokin kan hanya?”
Ta kalubalanci furucinta. A gare ta zuwa yanzu matsayin Abbas ya zarta wannan. He is
someone she respect most!.
Ya shiga zuciyarta da yawa, ta yadda har tunaninta ke canzawa a kanshi, zuciyarta na gayyatar
shi da wani matsayi mai girma. To ita kanta ba ta da ‘standing’, abin nufi. Ba ta san matsayinta
ba balle ta soma tunanin irin wannan, tana da aure ko babu? Ba ta sani ba.
Har ya kammala firfita shayin ya miko mata ba ta farga ba, ta yi nisa a tunanin ta.
Ya ce, “Lailah!”
Ta yi firgigit ta ankara. Ya mika mata shayin wanda ba ko tantama tana sha za ta amayar da shi.
Ya kan ce, “Ya fi babu dai tun da ko ya ya ne wani zai zauna a cikin hanjin cikinta”.
Abbas gwanin jinya da karfafa gwiwa, Abbas mai kyau, Abbas mai kirki…ya kan nuna mata
wannan ba komi bane, babu wanda baya fuskantar challange (kalubale) a rayuwa. And is up to
us to accept such challenges mu bita da duk fuskar da rayuwa ta zo mana.
Ya ce,
“Ni tashi na yi ba Uwa ba Uba Lailahhh. Haka nai ta gararramba a gidan wan mahaifina, sai dai
na kasance daga cikin hazikan yara, duk da gararramba ta.
Da na kare karatun sakandire gwamnati ta dauki nauyin karatuna a nan Ingila, kin ji abin da ya
rabo ni da gida.
Duk karshen shekara ina zuwa in gai da wan mahaifina. Da na kare karatun digiri na farko ya yi
min aure da diyarshi Hasina, muka taho nan tare, inda ta rasu a ya yin haihuwa.
Na zo gida Najeriya ne gai da Baffan nawa, na hadu da ke a filin jirgi”. Wannan shine
takaitaccen tarihi na.
Ba ta san me ya sa ba hankalinta ya kwanta da Abbas sosai ba, har take jin shine mutum na
farko da za ta kwaye ma cikinta, a kalla ko ba komi zai ba ta shawarar da za ta amfane ta, da
kuma yadda za ta yi ta gyara kurakurenta.
Ya ce,
“Uhm? Ina sauraron ki...?”
****
“A kullum ina tausar Sa’eed a kan rasuwar Zaliha, ina nuna mishi ya yi hakuri haka Allah ya
rubuta musu cewar ba mamallaka juna bane a gidan duniya.
Ya hakura ya nemi wata da ya kare NYSC ya yi auren shi. Duk da ina jin wani dan kishi-kishin
abin a raina.
Shakuwata da Sa’eed har ta kai matsayin da zuciyoyinmu suka soma karkacewa, al’amarin da
bamu tsammana ba (sha’awa). Na fahimci hakan ne daga yanayin kallon da Sa’eed ke min, da
wanda nima nake mayar mishi.
Ya zamanto ko abu Sa’eed zai karva a hannuna sai ya san yadda ya yi hannun shi ya gogi fatan
hannuna.
Muka soma wata irin rayuwa ta daban har ya zamanto Sa’eed babu inda ba ya shiga a dakuna
na ba tare da la’akari da halin da zai iya samuna a ciki ba.
Muka sake muka shantake muna abin da muka ga dama, sai dai bamu tava yin babban aiki ba,
wannan kam muna kula muna jin tsoro. Bamu tava yi ba, kuma bamu da niyya. Amma ‘yan
‘romances’ dinnan bamu dauke su komi ba.
Har ya kammala hutun zangon shi na farko na NYSC ya koma cike muke da kewar juna. Kamar
mu tafi tare.
Wasu watanni uku ris Mohammed ya kara a kan wadanda ya saba, suka zama shida ris kafin ya
waiwaye ni.
Bai san zuwa wannan lokacin ni tuni na rufe babinshi na daina kewar shi ba, don haka ya yi
mamakin yadda har ya yi ‘yan kwanakin da zai yi ya kare zai koma bai ji na yi ‘complain (korafi)
ba.
Bai sani ba ni tuni na samu madadin sa ba. Don haka lafiya-lafiya muka rabu wannan karon
yana ta sa min albarka.
Wata ranar lahadi Sa’eed ya zo har kofar dakina ya yi sallama, sanye nake da kayan barci
masu laushi ina shirin kwanciya barci.
Sai ya tsaya kallona galala, shi kadai ya san abin da yake kissimawa a ranshi. Ya kare ya ce.
“Aron wayarki nake so ki bani zan kira Hajiya wayata babu chaji”.
Na dauko waya na taso zan miko mishi ya hada dani ya rungume cikin wata irin rikitacciyar siga.
Na samu kaina da biye mashi, domin nima cike nake da kishirwar abin.
Cikin dan lokaci mune har a kan gado cikin al’amarin da ba zan iya fassarawa ba. Ban tava
samun ‘satisfaction’ (biyan bukata) da Mohammed irin yadda na samu a Sa’eed a ranar ba.
Wannan shine babban kuskuren da na tafka a rayuwata, ya kuma yi dalilin barowa ta gida, don
ban ga sauran amfani na a cikin gidan ba.
Da muka dawo hayyacin mu ne na fahimci aika-aikar da na tafka, ko in ce muka tafka.....”
Ta dakata ta share hawayen da ke kwaranyo mata, ko motsi Abbas bai yi ba, yawun bakinshi ya
dauke, ya kuma rasa wa zai bai ma laifin a cikin su duka ukun.
......Tsoron abin da muka aikata ya shige ni. Tsoron ingancin addinina da aurena ya addabe ni.
Tsoron mahaliccina da abin da za ya tambaye ni ranar da na gamu da shi ya shiga girgiza
zuciyata.
Mohammed kam bai sani ba, amma Ubangijina Ya sani, kuma ni da na aikata na sani. Sai dai
duk na dauki laifin na aza ga Sa’eedu, wanda kuma daga baya da na yi kyakkyawan tunani sai
na ga cewa dukkanin mu muna da laifi.
Na jima da neman gurbin karatu a wannan makarantar ta yanar-gizo ba tare da sanin
Mohammed ba, kuma ‘admission’ bai zo mini ba sai a dai-dai wannan lokacin.
Na duba gabas na duba yamma, kudu zuwa arewa, ban ga inda zan kai nadamata ba, baya ga
tafiya in barsu baki daya.
Don bani da bayanin da zan yi ma Mohd. Bani da bakin da zan fuskanci Ubangijina idan na
cigaba da zama dashi zaman zina. Amma shi din ai mai afuwa ne ga bayinsa. Don haka na
taho, har kuma hakan ya yi sanadiyyar haduwata da kai a filin jirgi.
Sai kuma ga wani sabon al’amarin.... ‘ciki’?” Ta furta cikin tashin hankali.
Bana tantama ciki na Sa’eed ne, don kamar yadda lissafin asibitin ya nuna, ya yi dai-dai da
ranar faruwar al’amarin Abbas........” Ta ci gaba da kuka.
Da da hali, da ya rungume ta ya rarrashe ta, shi kam tun da uwarshi ta kawo shi duniya bai tava
jin irin wannan kwamacalar ba, kuma iya amfani da hankalinsa da tunaninsa ya kasa rarrabe
wane ne mai laifi?
Ya gyara murya idanunshi sunyi jawur, ya zamo daga cikin kujerar da yake zaune, ya durkusa
ya zauna a gabanta, ya mika hannuwa kamar zai kamo hannuwanta sai ya fasa.
Cikin muryar lallashi ya ce, “Lailah! Ni dai shawarar da zan baki kada ki kashe rai. Ki ji tsoron
mahaliccinki, ki bar masa kudura da iradarsa.
Ni Abbas na ji nine uban dan da za ki haifa, ki haife ki bani zan yi mishi uba har karshen
rayuwata.
Babu wanda ba ya yi wa Ubangiji savo, dukkanin mu masu savo ne ta wannan hanyar ko ta
waccan.
Abin bukata shine, tsarkakken tuba da tabbacin ba za a sake komawa izuwa zunubin ba.
Sannan a ganina bai kamata ki yiwa Momin ki da ‘yan uwanki haka ba, yanzu gashi kin barsu
cikin tashin hankali.
Gara da a ce mutuwa ki kai sun san kin mutu, amma vatan dan mutum ba karamin tashin
hankali bane ga iyaye.
Ina mai shawartar ki da ki sassautawa zuciyarki, duk wani tsanani yana tare da sauki, kuma
babu wanda ba ya yi wa Ubangiji savo a bisa rashin sani ne ko akasi. Sai in ce ke kuma
wannan ita ce kaddarar ki”.
Hankalinta ya kwanta da nasihohinsa, amma a duk lokacin da ta yi tunanin wai dan kanin miji za
ta haifa, da aurenta, tana ji tana gani, zuciyarta kara dimaucewa take.
Ya ci gaba da tausarta da kalamai kala-kala, yana nuna mata wannan ba shi ne karshen
rayuwar ba. Ta ci gaba da istigfari ta fuskanci rayuwar dake gabanta.
[12/17/2019, 18:28] Takori: ****
Ya kwanta a hankali bisa madaidaicin gadonsa, ya rasa abin da ke damun sa. Wani al’amari ne
da bai tava faruwa da shi ba ke cin ransa.
Duk wani tunani nasa da ya mallaka ya dunkule ya warware a kan LAILAH. Bai tava tunanin
Lailan matar aure ba ce yake kauna, yana da burin ta zamo uwar ‘ya’yansa, ashe dukkanin su
basu da ‘yancin wannan al’amarin.
Ya yi parkin din motarshi kirar ‘Ferrari’ a kofar gida mai malalen siminti, irin gidajen nan na masu
kudin da can wani lokaci da ya shude cikin garin Jama’are.
Ya fito ya rufe kofar ya bude boot din motar ya yafito yaran da ke ta wasa a gida mai kallon su,
suka zo ya sanyasu suka kwashe kwandunan doya da dankali su kai cikin gidan.
Ya yi sallama a kofar dakin mahaifiyarsa, daga can ciki Hajiya Baida’u ta amsa tare da yi mishi
kallon kauna, kafin ta amsa sallamar shi. Ya zare takalman shi ya sanya kai cikin dakin.
Ya samu kujera mai fuskantar mahaifiyarsa ya zauna, kai da ganinsa da kuma irin zaman da ya
yi rigija…. ka ga wanda kwanciyar hankali ya yi wa karanci.
Ta tura mishi kwanon gurjiyar dake gabanta kamin ta mike ta je kitchen ta shiryo masa abinci
mai rai da motsi.
Sai da ya ci abincin ya sha ruwa kafin da ta yi masa wani irin kallo ta girgiza kai.
“Anya Mamman! Kana nemawa kanka sauki cikin tunanin yarinyar nan? Na rantse da Allah ba
ta sonka, da tana sonka da ba ta yi maka wannan abun da ta yi ba, data tabbatar zai daga
maka hankali, tunda tana sane ta yi tafiyarta ba shi ke nan ba?
Kiri-kiri ta nuna maka ta gaji da zama da kai ne don baka haihuwa, shi ya sa ta yi tafiyarta
amma ka bi ka kwazzabi kanka banza da wofi, sai ka ce dan kankanin yaro ne ya vata. Kana ta
asarar kudinka a cigiyar banza.
Tsiyar auren ‘kwara’ kenan, don ba za su zauna ba. To yaran yanzu ne idan kun so auren mace
kamar da ya so fitowa cikin mahaifiyarshi, ba za ku yi aure a gida ba inda a ka san mace, aka
san asalinta, a’ah, ku sai kyal-kyal banza”.
Maganar Hajiya ta shige shi ainun, da gaske Lailah ba ta sonsa! Ko ta so shi a baya, yanzu ta
daina!! Da tana sonsa da ba za ta tava gajiya da zama da shi ba, kowanne irin hali ne da shi
kuwa.
Balle kuma yana iya kokarin sa wajen fita hakkin ta. Da gaske ne Lailah gajiya ta yi da zama da
shi don rashin haihuwa shi ya sa tai tafiyar ta?
Zai so ya ganta a wannan lokacin, ko don ya yi mata wannan tambayar.
Hajiya ta gyara zamanta ta ce,
“Ban da abinku na ‘ya’yan zamani da ba a yi muku gwaninta, da sai in ce mai zai hana ka yi
auren ka ka huta?
Ga nan ‘yar kanin mahaifinka A’isha, ta gama karatun digirinta na farko a jami’ar Bayero, mai zai
hana ka tuntuve ta?”
Ya yi ajiyar zuciya abin tausayi, ya ce, “Hajiya duk yadda kika ce dai-dai ne”.
Ta ji dadi, ta shiga sanya mishi albarka.
A ranar ya soma zuwa wajen A’ishar, doguwa, baka, mai kyakkyawar sura. Ya yaba da
hankalinta da nutsuwar ta, don haka ya sakarwa Hajiyar shi bakin aljihu ta soma shirye-shiryen
aure.
A karshen satin Sa’eed ya zo, nan ya tsinkayi labarin auren. Ya samu dan uwanshi a gidansa da
yammacin ranar asabar.
“Yanzu daga Jama’are nake, Hajiya ke gaya min wai ka amince ka auri A’isha”.
Ya ce, “Eh, haka ne, Lailah ta yaudare ni Sa’eed, ta yadda har ban san ba ta kauna ta ba sai
yanzu, da tana kauna ta da ba ta yi min abin da ta yi min din nan ba”.
Sa’eed ya ce,
“Ba yaudara ba ce Yaya! Idan ka dubi wasikarta da kyau, za ka fahimci halayyarka ne ba ta so.
Sai dai nima na yi mamakin dalilin da ya sa ta zavi tafiya, fiye da ta nemi saki”.
Ya ce,
“Koma dai mene ne ni aurena zan yi, tukuicin kaunata gareta kenan, to ta je, Allah ya ba ta
sa’a”.
Sa’eed ya ce,
“To idan kuma ta dawo fa?”
Ya ce,
“Bana jin Lailah za ta taba dawowa gare ni. Da za ta dawo, da zuwa wannan lokacin koma
mene ne in ta yi don ta hora ni ko don na gyara kuskuren da nake mata da tuni ta dawo”.
Sa’eed dai ya rasa abin cewa, can karkashin zuciyarsa kuwa nadama ce fal, don ya san shine
silar wannan al’amarin.
A wani bangaren tunanin ranar da Allah zai tona asirin cin amanar da ya yi wa dan uwansa mai
kaunarsa yake yi, don ya san ba shi da fuskar da zai dube shi daga ranar, ya kuma tabbata ko
ba dade ko ba jima wata rana Allah zai bayyana al’amarin.
****
Ya kwankwasa kofar ta taso a hankali ta bude, sanye da bakar jallabiya kirar Oman a jikinta.
Ya shigo rike da ledar magunguna a hannunshi na dama, ya yin da hagun ke rike da wata ledar
cike taf da ‘ya’yan inibi.
Suka yi ma juna murmushi a takaice, ya ja kujera ya zauna ita kuma ta koma bakin gadon tana
fuskantar sa.
Ya ciro magunguna a leda ya valla ya mika mata tare da dauko mata gorar ruwa mara sanyi a
firinjinta.
Ta amsa ta soma hadiya, ya ce,
“Lailah, yau dai ki daure ki shirya muje makaranta, don na ga jikin da sauki. An kafe maku
time-table din edam tun shekaranjiya”.
Hanadi, mutuniyar Somalia wadda dakinta ke kallon na Lailah ta yi masu sallama ta shigo, ta
samu gefen gadon da Lailah ke zaune ta zauna suka gaisa.
Ta ce,
“Kwana biyu bana ganin ki kin fito ko kin shiga kitchen, shine na ce bari in zo in ga ko lafiya?”
Tana maganar ne cikin harshen Turanci. Cikin jin dadin kulawar da ta nuna a gare ta ta ce.
“Wallahi kuwa, ina fama da zazzavi ne”.
Ta ce,
“Ayya! Ga shi nan duk ya ramar da ke, Allah ya kawo sauki”.
Su duka suka ce,
“Ameen”.
Suka dan tava hira Abbas bai tofa musu ba, sannan ta tashi ta yi musu sallama ta fita.
Shi ma fita ya yi don ya ba ta dama ta shirya. Ta dauko farar suwaita ta sanya, ta kawo doguwar
‘coat’ har gwiwarta ta sanya tare da dogon wandon ‘cherokee jeans’, ta sanya socks na hannu
da na kafa da rufaffen bakin takalmi maras dunduniya.
Ta dauki katuwar jakarta mai dauke da littattafanta ta rataya, ta janyo kofar dakinta ta sa makulli
ta rufe.
Ta gangara kasa dakin Abbas, ta kwankwasa ya fito shi ma a shirye cikin DKNY, (trouser and
shirt), da bakar suwaita a kai. Ya yi matukar yin kyau, suka jera suka fita. Suka tsaya a ATM na
bankin ‘Lioyds’ ta dauki kudi suka karasa makaranta da kafafun su.
Da suka dawo suka tsaya a kantin ‘Morrisons’ dake nan cikin unguwar su (Acton) suka yi
‘shopping’ suka dawo gida.
Haka Lailah ta ci gaba da rainon cikinta da taimakon Abbas, tun tana damuwa da bakin ciki har
ta daina.
Yau da lafiya gobe babu, haka ta daure tana karatun ta. Sai da cikin ya shiga watanni biyar
sannan ta samu lafiya, kai in ka ganta a wannan lokacin ba za ka ce ciki gare ta ba, saboda
yanayin shigar ta na kaya masu kauri.
Allah sarki Abbas, tun daga wannan lokaci ya soma sayan kayan jarirai yana tarawa (unisex).
Lailah dai ba ta tava sayen komai ba, ita dai ta mika wuya ga duk yadda rayuwa ta zo mata, don
ba ta da tsimi ba ta da dabara.
Abbas ya samu aikin koyarwa (temporary) a wata makarantar sakandire (private), ya zamanto
Lailah ta daina tava ajiyarta ta banki, ya tsaya mata a kan komi, itada jaririnta dake ciki.
Katon na locozade, katon na fresh milk, cret din kwai,