Showing 3001 words to 6000 words out of 56966 words
Chapter 2 - WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf
gani ba) duk da ita ba ta yi kwalliyar ba.
Karewa ma hawaye ne sharkaf, jave-jave a idanunta. Haka ba ta nuna kowacce gava ta jikinta
ba, in ka dauke shatin fuskarta.
Sai dai kana iya hango kwantaccen gashi baki wuluk mai sheki da walkiya daga saman
goshinta, sakamakon mayafinta da ya dan zame baya cikin rashin saninta. Wanda ke nuni da
ba bafullatana ba ce.
Wannan kyan ya kere na fulfulde, kyau ne da launin mutane biyu ya haifar, wato baki da fari
(half - caste) da aka fi sani da ruwa biyu, daga uwa da uba.
‘Yammatan suka iso layin da suke tare da dan tebirin su mai tayoyi (troller) mai dauke da duk
wani nau’i na ababen jika makoshi, tun daga kan shayi, wine (giya), coffee, ruwa, jus da
kwalayen taba nau’i-nau’i.
Cike da ni’imtaccen murmushinsu suke tambayar Lailah da ke kife da kai abin da take so.
Ko kallon su ba ta yi ba. Dan sa-idon nata, tuni ya ari bakinta ya ci mata albasa, ya ce a bata
ruwa mai sanyi ta jika makoshinta.
Daya daga cikinsu ta ce,
“Hala amarya ce? Honey moon in the heart of England?”
Murmushi Abbas ya yi.
“Yap....... but we ‘ve a little misunderstanding (mun samu ‘yar kankanuwar rashin fahimta) shine
take fushi, irin na mata da miji, kin gane?”
Ta yi murmushi ita da abokin tafiyarta ta ce.
“Wannan ba wani abu bane, abu ne da ke faruwa a cikin SOYAYYAH. Idan babu irin wannan
babu ingantacciyar soyayyar a zuci. Cool down my friend……”.
Ta fadi tana mai dafa kafadun Lailah. Har da dan jijjigata.
Mamaki da haushi ne suka kashe mata baki ta kasa cewa uffan har suka wuce, bayan sun cika
mata dan kofin su da ruwan abarba mai sanyi.
“Kulawa ma yabawa ce”.
In ji Malam Bahaushe. Idan Abbas na tunanin irin shisshiginsa zai yi tasiri ya samu kulawar
Lailah, wadda ke kallon dukkan maza ‘naked’ (tsirara) babu sauran mutunci babu sauran
aminci da su a idanun ta ya yi kuskure. Har suka sauka a Heathrow ba irin shisshigin da bai
mata ba, amma uffan ba ta ce mishi ba. Hakanan bata kalleshi ba. Da yawan ma’aikatan jirgin sun yi zaton da gasken mata da miji ne duk da yadda fuskarta da
ma zuciyarta suke a jagule.
Don da za su fita jirgin ma’aikatan na ta yi musu fatan alkhairin ‘honey moon’ ne cikin kasar su
(kamar yadda ya ce) yana amsawa a dokance. Yana binta kamar jela, kamar wani ‘body guard’ ,
ko ko mai take mata baya, da kula da al’amarinta.
Duk wannan na faruwa ne cikin Air-port din ‘Heathrow’ cikin dakikan da basu fice mintuna talatin
ba.
Da suka zo kanta wato wajen tuhumar ingancin visa na karshe ga wadanda ba ‘yan kasa ba,
wanda daga shi sai shigewa cikin garin London. Ya fahimci Lailah ba ta tava shigowa Ingila ba,
domin daga ganinta ta fara tsorata daga tsabar binciken da ake yi mata, har ta zamo perpleded
(rudaddiya).Ya ce sai ta tsallake wannan ‘inter-view’ din tukun shine na karshe. Tare da gaya
mata cewa ta kula sosai wajen basu amsoshin tambayoyin duk da suka yi mata, ban da dadi
ban da ragi, domin hakan na iya janyowa a hanata shiga.
Hankalin Lailah ya kai kololuwar tashi, idan da abin da yake na karshe da ba ta son ji a wannan
lokacin, to komawa gida Najeriya ne. A dai wannan lokacin da ba ta san matsayin rayuwarta ba.
Ta zo ne domin yin karatun da za ta yi wa kanta hukuncin da addini ya tanadar a kanta.
To amma why a Britain?
[12/17/2019, 17:50] Takori: Idan ilimin addinin musulunci ne ai yana kasar musulunci. Wannan
kuma yana daga cikin dalilanta na son vatar da hankalin kowa nata daga tunanin inda take. Ta
san nan ne kadai waje na karshe da iyayenta da shi kansa ba za su tava tunanin za ta zo ba,
tunda ba ta tava zuwa ba. Kuma bata da kowa. Sai dalilinta na biyu shine, tana da masaniyar cewa babu kasar turan da ke zaune da al’ummar
musulmi lafiya irin Ingila. Kasa ce da ta bai wa kowa dake cikinta ‘yancin yin addininsa da
walwalarsa, ba tsana ba tsangwama, idan har ka bi ka’idojin da ta shimfida maka. Wannan
shine babban dalilin ta na zavar kasar Ingila a matsayin mafaka ga ruvavviyar rayuwarta.
Lailah ce tsaye can gefe a kanta tare da (UK Boarder Agency) masu binciken ingancin bisarta
na karshe kamin su barta ta wuce. Tana amsa tambayoyi na karshe. A nutse take tsaf, cikin
kamalarta da voye vacin ranta, tana mai amsa dukkan tambayoyin da a kai mata daki-daki da
tsaftataccen turanci mara amo. Sun gamsu, sun yarda da zamanta cikin kasarsu baya nufin
ha’inci ko vad-da-kama, ko kuma ci - da - gumin - wani. Saima su da za su kara bunkasa tattalin
arzikinsu daga asusunta wanda ke cike taf da (sterling pounds).
To nan suka fi kauri, don haka suka daga mata kafa ta wuce. Ta fesar da ajiyar zuciya mai
nauyi, domin ta riga ta tsorata da tambayoyin ka-ka uwar ki ta haife ki da suke antayo mata.
Ta yi tunanin idan aka ce ta koma gida a yanzu ina za ta dosa? Ba ta fata, sai ta yi wa kanta
ilimin da zai tallafi gurvatacciyar rayuwarta.
Already shi har ya dau jakarshi. Ta dan yi mintuna kamin tata ta iso ta dauka. Suka jero gwanin
ban sha’awa kamar mata da mijin gaske zuwa bakin titi.
Hadaddun Jeep-Jeep ‘yan gujif-gujif amma wai tadi ne (drop), su Laila ta fara yin tozali dasu a
jere raras suna tsimayen mai hawa.
In kin san wani abu wai shi dacewa, wato (matching) na karshe, to Lailah da abokin tafiyarta ne,
wanda har zuwa wannan lokacin ba ta yi mishi wani kyakkyawan kallo ba balle ta tantance
kamanninsa.
Shi kuma haka nan ya bi ya nace ya manne kamar wani tsohon maye yana bibiyarta kamar
bindi. Ba tare da damuwa da halin ko in kulan da take nuna masa ba.
Ya lura ba ta cikin cikakkiyar nutsuwa, haka nan ba ta san ko ‘ina ba. Sai dai kuma ba ta da
duhun kai, don ba ta tambayi kowa ba. Ta san iliminta zai mata jagora a ko’ina.
Ta karanta adireshin makarantar da ta zo, (20 Creffield, Earling, London), ta maida takardun
inda ta dauko su a jakarta, ta nufi daya daga cikin tasin.
Tun kan ta karasa wani dan motsattsen Bature ya iso gare ta ya amshi jakarta yana kokarin
sanyawa a boot.
Hannuwanshi biyu ya sanya ya ciro jakar daga boot din tasin, ya ja Baturen gefe yana
murmushi ya ce da shi cikin harshensa.
“Kyale ta fushi take, ka san amare abu kadan sai su hau, su yi fam!”
Baturen ya kyalkyale da dariya ya ce, “To ai kai ma abokina amare lallava su akeyi”.
Ya ce, “Ina lallava ta tana kara hawa sai ka ce alkubus, ka gane rigima ce da Madam, ta fi son
mu sauka a DUNDEE ni kuma na fi son London. Shin akwai inda ya kai London dadin ‘honey
moon’ ne a Birtaniya?”
Da sauri Baturen ya girgiza kai ya ce, “A’ah, garin sarauniya ai babu kamar shi a duk fadin
Ingila”.
Ya juyo ga Lailah yana murmushi wadda tuni ta yi mutuwar tsaye.
“To kin ji sai ki daina fushi, ki daura aniyar zaman London da kin ki da kin so. Ina da ‘oyster’
(katin hawa jirgin kasa) har biyu, zan baki guda. Gara mu bi ‘train’ yafi saukin kudi.Wuce muje
Ma sis..........”
Wannan karon da Hausa yake magana don kada mai tasi ya fahimce shi. Ya zaro fam ishirin
cikin wallet dinshi ya mika ma mai tasi, amma ya ki amsa, su kai sallama ya yi gaba.
Ba ta da zavi ban da ta bi shi, domin da jakarta da nashi ya hada ya wuce.
Ba ta tava ganin mutum mai shisshigi irin wannan ba. Haka ba ta tava ganin mutum mara
zuciya irin shi ba.
“Uffan ban ce maka ba, kallo wannan baka ishe ni ba. Amma ‘still’ baka fasa naci ba”.
Ta furta cikin takaici, tare da jan wani matsiyacin tsaki, “Tsuuut!”
Ya ji sautin tsakinta, amma bai san ko me ya sata yin tsakin ba. Ya murmusa har cikin ransa ya
ce.
“haka nake kiyi hakuri dani, naci akan abinda na kwallafawa rai, nake kuma son sani. Wanda
akafi sani da ‘curiosity’. Am curious about you! Yanzu meke damunki? Yunwa ko gajiya?
Kada ki damu, I’ll cook deliciously for you........ (zan miki girki mai dadi, ni gwani ne wajen girki,
lokacinda matata ke raye).
A mamakance Lailah ta cira kai ta dube shi, wannan karon cikin ido. Ta tsorata, ta mamakantu,
haka ta firgita da abin da ta gani cikin kwayar idanunsa (Mohammed sak!).
Amma hakan bai kada ta ba kamar zallar kyau da haiba irin na wannan mai naci. Duk da cewa
baki ne amma bakin shi mai kyau ne. Ta ko’ina ba ta inda Ubangiji ya rage sa.
Ba ta san yaushe murmushi ya suvuto daga bakinta ba. Karo na farko da ya ji sautin muryarta
ba cikin kuka ba.
Ya lumshe ido yana bude su dukka a kanta, sun kada sun yi jawur. Wannan karon sautinshi ya
yi kasa very cool! Ga dukkan alamu tunanin mutuwar matar ya tava zuciyarshi.
A hankali ta ce, “I’m sorry”.
Ya ce, “Na gode”.
A marairaice ya ce, “Ki yi hakuri ki karve ni LAILAH”. (Ya ga sunan ne a jikin passport dinta). Ko
da a matsayin abokin tafiya ne, bana nufin komai dake sai alheri Lailah. Lailah ina so na
taimaka miki ne, ta wani fannin in taimaki kaina. Kin amince dani Lailah?”
Ta karaya, amma bata son nuna karayar tata a kan MAZA. Tana da tabon su, tana da danyen
mikin su cikin ranta, tana da mummunan kullaci a kan al’amarin su;
Sune suka rabo ta da iyayenta da basa hada kaunarta da ta kowa. Sune suka rabo ta da
mijinta da aurenta. Sune suka rabo ta da ‘yan uwanta da aminanta...... Sune.....sune.....sune
suka yi wa zuciyarta gyambo da har abada ba zai warke ba.
Sune suka yi mata miki mai rudani, suka sanyata cikin rudanin rashin sanin sahihanci da
ingancin addininta......
In haka ne ita wace irin wawuya ce da za ta amince ta sake fadawa a tarkon su haka ‘so early?’
(da wurwuri?)
Ta girgiza kai ta furta mishi da karfi, “Never! (Fau-fau). Babu ni babu Da Namiji!”.
Ya yi saurin juyowa idanunshi sun kada sun yi jawur, yana son tantance sanadin wannan
ANGER (fushin) da ke cikin muryarta.
“Why Lailah (me ya sa)?” Ya bukata.
“Ai ba duka muka taru muka zama daya ba. Kowa sunan shi yake amsawa. Kada kiyi mana
jimilla a rashin kirkin, wannan rashin adalci ne!”.
Ta soma kokarin kwatar jakarta tana magana, wannan karon cikin kuka.
“Am not your wife (ni ba matarka ba ce), so why the disturbance? (meye dalilin wannan
takurawar?)
Ka kyale ni in yi tafiyata, ka kama hanyarka in kama tawa, ka yi wa Allah ka rabu dani........”
Kuka ya ci karfinta.
Karfinta ya kare domin ta kasa kwatar jakar. Karfin mace, da karfin namiji. Balle zabgegen
mutun irin ABBAS. Wadanda irin su tsiraru ne a cikin al’ummah.
Sai ta tsuguna a nan kan kafafunta ta sa mishi kuka mai gigitarwa, tana rokon shi Allah da
Manzon shi ya ba ta jakarta ya yi tafiyarsa ya kyale ta.
Shi ma sulalewa ya yi nan a gabanta a kan gwiwoyinsa idanunshi a rikide, amma ba kukan yake
ba.
Numfashinshi ke gwagwarmaya da sauri da sauri. Ji yake in duk duniyar nan za ta taru a kansa
ba za ta raba shi da Lailah ba!.
“Hanya mai hadin zumuntar dole….”, in ji ‘yan Magana. Lailah ta gamu da gamonta. Ta ci
kukanta ta koshi, ta tabbatar ba zai rabu da ita ba sai dai su kwana a nan. Ta yi tunanin hada
shi da ‘yan sanda kawai su yi masu katangar karfe. Daga baya wata zuciyar ta ce da ita, “A kul,
shi din kin san wane ne?” Bai yi kama da irin mazan da mace za ta wulakanta ta kwan lafiya ba,
bai yi kama da wulakantaccen mutum ba. Haka bai yi kama da wadanda ‘yan sanda za su
girgiza ba, tun da kasa ce da kowa ke da ‘yancin kansa.
Ba ta da zavi ban da dangana, ta yi gaba tana huci ya bi ta a baya yana murmushin cin nasara.
Suka gangara ta liftar kasa zuwa ‘Rail-Station’ na Heathrow, suka yi amfani da katunan Abbas
na hawa jirgin kasa suka hau jirgi mai zuwa cikin ‘Central-London’.
***
12/SAFAR HIJIRIYYAH
Cikin jerin gwanon masu saukowa daga matattakalar jirgin ‘Royal Air Moroc’ har da Engineer
Mohammed Bauchi, fari sol da shi bafulatanin Jama’are, ga dukkan alamu babu tambaya, cikin
caftan na ‘ash colour’ shadda mai taushi da walkiya. Agogon (RADO) baki sai sheki yake cikin
tattausar fatar hannunshi da bakin lallausar gashi ya baibaye. A very serious person (wanda babu alamun wasa cikin al’amarinsa), wato irin mutanen nan
masu wuyar sha’ani da rashin walwala. Sai dai fa in ka san wata kalma wai ita ‘aji’ na karshe, to
Mohd. ya mallaki dukkanninta.
Dan kimanin shekaru 35, Mohammed, yana da tsayi sosai da lange-langen jiki na fulanin usli,
wadanda suka jiku suka zurfafa suka gogu cikin ilimin addini da na boko.
Ga wanda duk ya san Mohammed Jama’are, ya san shi da wannan halayyan nashi na
(seriousness), watau daukar abinda ke gabanshi da muhimmanci a kan komi. Babu abin da
yake bai ma lokaci kamar aikinsa da abubuwan da ke gaban shi, na ci gaban rayuwar shi.
Tun kan ya idasa saukowa daga matattakalar ya zura hannu cikin aljihun kaftaninshi ya fiddo
wayarshi ya kunna, yana kiran kanin shi Sa’idu ya zo ya tarbe shi.
“Big Bro. isowa haka unexpected?”
Ya fada cikin kasalalliyar murya.
“Da tun jiya ka sanar damu, yanzu haka ina cikin Jama’are, Inna ba ta jin dadi”.
“Ow.k, ba matsala, bari in kira Lailah, ai tana gida ko……?”
Shuuuu...... ‘network’ ya katse, don haka bai ji amsar Sa’id ba.
Ya lalubo lambar ya kira, sunan ‘eclairs’ ya soma yawo a ‘screen’ din. Ta yi kara har ta gaji babu
agaji.
A karo na biyu ya sake kira. Wannan karon ma ta yi ta vurarinta har ta gaji, ‘eclairs’ ba ta agaza
mata ba.
Cike da kosawa ya sake kira a karo na uku, ta yi har ta gaji ta tsinke don kanta. A serious
person, abinki da dama ya ya lafiyar giwa? Nan da nan ya kufula, gaba daya ya kashe wayar
don haushi, ya figo jakarshi zuwa harabar ‘air-port’ ya samu achava ya dane, mai machine ya
rike jaka a gabansa, bai tambayi ba’asi ba ya figi babur, ga dukkan alamu wannan oga a kule
yake, don haka bai tambayi inda za a ba sai da ya mula don kansa ya fada mishi.
Gidan na daga jerin farko-farko na gidajen unguwar (Fati Mu’azu Links) cikin Bauchin
Yakubu, gida ne ‘flat’ karami hawa daya ma’abocin wadatar shuke-shuken furanni masu launi
daban-daban da kamshi daban - daban. Karamin gida ne da ya kunshi duk wasu nau’o’in
abebaden jin dadin rayuwa cikin tsari da sanin ciwon naira. Abin nufi, babu almubazzaranci, babu fariya, haka babu son nuna isa. Komi ka gani cikin gidan
mai amfani ne, haka ba a yi dakuna rankatakaf ba adadi ba.
Kwata-kwata dakuna ciki uku ne da makeken falo, sai (boys quater) daga waje da (study room)
mai kunshe da littattafan da suka shafi mazauna gidan.
Maigadi ya saki baki bude, ganin maigidansa na sauka daga kan dan achava da jakar kayansa.
Ya ciro kudi ba tare da ya kirga ba ya mika mishi ya wuce yana godiya.
Malam Surajo bafullatanin garin Dambam ta jihar Bauchi, kuma amintaccen maigadin maigidan,
ya karvi jakar uban gidansa ya yi ciki da ita ba tare da ya jira ubangidan ya gama kiraye-kirayen
wayar da yake yi ba.
Ya yi matukar mamakin ganin motar matar gidan na nan. Rufe cikin tamfol, sai dai ga dukkan
alamu an jima ba a yi amfani da ita ba, sakamakon kura da ta yi futuk ita da tamfol din.
Motoci uku ne dama a ma’adanar gasunan. Wanda ke nufi tana cikin gidan, tana ganin kiran
wayarshi amma don iya shege irin nata ta ki amsawa da gangan.
Ya yi kwafa kana ya tura kai cikin gidan. Ko’ina a bude, ba a sanya makulli ko daya ba.
Sai dai fa ko’ina futuk yake da kura kamar babu halittar dan Adam a gidan. Tuni Malam Surajo
ya aje jaka ya fice domin da alama ogan na cikin masifan nashi da ya saba.
Yana tsoron kada bai kar zomo ba a ba shi rataya, don haka ya yi hanzarin daukar buta ya zaga
bayi domin gabatar da alwalar sallar azuhur.
Niyyarshi yau sai Allah kadai zai saukar da shi daga fushin shi, duk dadin bakin nan nata…, duk
kissa da kisisinar nan nata….., duk lailaya da rarrashin nan nata……, duk taushin hannuwan
nan nata........da tausasan levvan nan nata, masu mantar da da namiji duk wani jin kai, takama
da mukaminsa. Yau sun yi kadan su sauke fushin takwaran Manzo. To amma fa ko wajen zama bai gani ba a dai wadannan fututuk din ‘leather’ din masu kama da
an yi wata ba a hau ba.
Babu motsin kowa, babu motsin komi balle ‘yan wake-waken nan nata na zabiya ‘Nancy
Agram’ idan tana ‘yan girke-girke da kaye-kayenta cikin kitchin.
Jikinsa ya soma yin la’asar. Kai tsaye ya fada kitchin babu ita, ya banka dakin barcin su.... a nan
ne idanuwanshi suka gano mai abin al’ajabi.
Kafatanin kayanta da ke cikin ma’adanar kaya gasu nan baza-baza a kan gado. Ga alama an
kwashe