Showing 15001 words to 18000 words out of 39674 words
Chapter 6 - HAUWA KULU Yar Cikin Badala Part 1 BY TAKORI.pdf
ba zaa tuhume shi ba, tunda ya tafiyar da
komai a kan kaidar aikin sa ne, amma IDO fa ake zance, wannan kwayar tsokar guda biyu mafi
amfani da muhimmanci ga halittar dan adam, sannaan in har kana da zuciyar yan adamtaka a
cikin kirjin ka da humanity a tare da kai, dole zuciyar ka ta tabu, da ganin yadda fuskar Innar
Hauwa ta shiga tashin hankali a lokacin da Hauwa tace,
bata ganin komai a gabanta sai duhu.
Wanda tayi ta kokarin danne tashin hankalin data shiga din saboda shi. To shi tashi zuciyar
ba tabuwa kawai ta yi ba da tausayin su da disappointment akan aikinsa, ta kekkece ne, sannan
ta tsatstsage ta yayyage ta yagalgale (into pieces at the same time). Ta yadda a gaban Innar
Hauwa duk dauriyar da yake yi sa sai da idonsa ya kada, kwalla ta cika idonnasa, a fakaice ya
yi kokari maida kwallar, ta hanyar juya musu baya ya zuba dukkan hannayen shi cikin aljihu
yana maida kwallar sa, bai san Innar ta gane halin da yake ciki ba.
Hakan ya faru ne lokacin da ya ji Hauwa tana cewa.
Shike nan yanzu Inna sunana Makauniya? Ba zan sake ganin fuskar ki data Baban mu
ranar da ya dawo gare mu ba? Kema na daina ganin ki kenan daga yanzu?”
Yana iya tuno kalaman Innar Hauwa gare shi, da ta ga yasa hankici yana tsane kwallar
da yake ta hadidiyewa cikin idanun sa a wayance, yanzu kam tafi karfin sa, ta baiwa kanta yanci
ta digo, a lokacin yana rubutu cikin fayil din Hauwa sai hawaye ya diga a kai, wannan ya faru a
kan idon Innar Hauwa. Sai Innar Hauwa ta bagarar da tasirin maganganun Hauwa suka yi mata a ranta, ta maida
kulawarta a kan shi inda ta dube shi cikin lallashi tace Haba likita? Kaida zaka bata karfin
guiwa? Shi Dan adam ai baya tsallake kaddarar sa. Ita Hauwa-Kulu kaddarar ta kenan.
Abin yi a yanzu gaba dayanmu shine mu yi mata fatan Allah yasa makanta ta zamo kaffara a
gare ta. Idan makantar nan jarrabawarta ce ta dan wani lokaci Allah ya yaye mata ya bata ikon
cinye wannan babbar jarrabawa, idan kuma ta har abada ce Allah yasa ta zamo silar shigarta
aljannah. Nakasa ai ibadah ce ga wasu kebabbub bayin Allah!.
Amma duk da tawakkali irin wannan wanda Innar Hauwa ta nuna, Dr. Sarham ji yake
yana blaming kan sa, kamar rashin kwarewar sa ce ta saka Hauwa a wannan halin na rasa
abinda yafi komai dadi ga rayuwar mutum, wato idanun ta.
Zai fi yarda idan aka ce sakacin sa ne, laifin sa ne, rashin kwarewar sa ko iyawarsa ce. To ko
dai gaskiyar mutane ne da suke cewa yayi kankanta da zama mai ceton rayuwar idanun
alummah?
Yaushe tasirin maganganun jahilan matan nan magulmata zai bar ransa ya sake ne? meyasa
ma kunnen sa sarkin ji, ya zuko masa abinda ba alkhairi bane a gareshi kuma wanda zai dame
shi?
Don haka koda ya baro su a asibitin ya dawo gidan su a ranar, wato gidan mahaifin sa,
da matsanancin duhun zuciya ya shigo, mahaifiyarsa kanta ta fahimci cikin matsananciyar
damuwa Lelen Abba yake. Tun daga bakin kofa kanwar sa Sumayya ta soma tarar sa da zance
yadda suka saba saboda shim aba laifi akwai hira musamman da kannen sa, Sumayya tana
gaya masa ta yi (passing exams) din ta, kawai ya zo ya bata kyautar da yayi mata alkawari bata
son a bata lokaci har kyautar tabi ruwa tunda shi yayi alkawari. Amma ga mamakin Sumayya
yau Lelen na Abba ko kulata bai yi ba, yayi fuska kamar ba shi ba, don ko kallon ta bai tsaya ya
yi ba, balle ya bata lokaci wajen taya ta murna yadda ya saba in taci na daya a kowanne
zangon karatu, balle har ya ce su fita kingsway ta zabi ‘gift’ din da ya yi mata alkawarin.
Kawai sai yasa kai ya wuce zuwa dakin sa abinsa, yana cewa a ransa baki da matsala, ko
sannu da gida yau bai iya ya yi mata ba itada sauran jamaar gidan bakidaya.
Sumayyah bata daddara ba, ta sake kwasar faranti data shake da abinci ta biyo shi da
abincin rana har dakin sa. Da yake ta gan shi cikin damuwa sai tayi tunanin yi masa abincin da
ta san ya fi so, wanda dole zai kula yayi godiya, wato tuwon alkama miyar kubewa busassa.
Miyar ta ji busashshen kifin banda da cryfish, ga lafiyayyen farfesun kayan ciki ta hado masa da
shi da yaji kayan kamshi da attarugu, komai zai ci sai ansa tarugu da tafarnuwa, sune abinda ke
sawa yaci abinci sosai ta sani, duk ta jera a kan tray ta biyo shi da shi har daki.
Sai ta samu kofar tasa ma a kulle da mukulli, wato ya kulle kan sa, don baya son kowa ya
dame shi. Musamman ita Sumayya sarkin naci da zuba zance, ya san saita biyo shi, saboda da
shi kadai take shiri ta kuma fi sabawa cikin gidan, bata iya zama idan ba kusa da shi ba.
Wannan kulle kan sa da yayi a daki tun dawowar sa gida da hantsi har bayan laasar ya dami
mahaifiyar sa Barr. Mai shariah Haj. Maimuna (Mama inji yaranta). Har bayan laasar suna zuba
idon ganin fitowar sa shiru suke ji, ta tambayi Sumayyah ko ya ci abincin ranar data kai masa?
Nan take gaya mata cikin tata damuwar, ai Mama ko bude dakin bai yi ya dauka ba, dazu na kara dubawa na ga abincin yana nan a
bakin kofa inda na ajiye masa”.
A lokacin Yayar Sumayyah mai bin Dr. Sarham a haihuwa wato Aunty Surayyah ta dawo
gidan, daga gidan Kakar su Hajiya Kulu. Ba jimawa mahaifin su ma ya dawo daga cikin
makaranta inda yake koyarwa wato Prof. Abbas Shanono, nan gidan ya idasa cika ya zama
full-house yadda yake a kowanne yammaci in sun dawo daga sabgogin su. Prof. Abbas ya tadda su jigum jigum a falo wato dai damuwar Lelen Abba (Sarhamu) ta taba
kowa. Don an yi bugun duniya bai bude ba, da Sumayyah ta dame shi da nacin rokon ya bude
kofa ya dau abinci, a fusace yace mata in bata bar masa bakin kofar dakinsa ba zai fito ya yi
kasa-kasa da ita a wurinnan. Yau ban ga Sarham a masallaci ba ko bai dawo bane? In ji Abba Prof. ya fada yana
nazarin yayan nasa mata guda biyu da mahaifiyar su wadanda duk suke cikin damuwar abinda
ke faruwa da babban Yaya.
A kaidar Abba Prof. idan ya dawo gida daga cikin Jamia kullum, kasancewar suna zaune ne
a cikin rukunin gidajen manyan malamai na sabuwar Jamiar Bayero, kafin ya shiga gida
masallaci yake fara zarcewa wanda ke kofar gidan sa, mafi yawancin lokuta a can zai tadda
Sarham ya riga shi isa, sabida baya wasa da bin jamI, kuma sautari ya kan riga shi dawowa,
zasu hadu a can, su bi jami tare, ba zasu shigo gida ba sai bayan laasar.
Amma sabanin kullum yau har aka idar da sallah bai ga Sarham ba. Wannan abu ya
dugunzuma shi, don ya jima rabon da yaga ranar da yana gida bai je masallaci haka kawai ba.
Mama ta gaya masa yau sun rasa gane kan sa, ya shigo cikin damuwa daga wajen aiki, ya kulle
kan sa tun dazu, har ya kusa dukan Sumayya da ta dame shi sai ya bude ya dauki abinci. Bata kai ga rufe bakin ta ba sai ga Dr. Sarham ya fito daga dakin sa da saurin sa da
hanzari, da mukullin motar sa a hannun sa, tun kayan dazun ne a jikin sa bai canza su ba,
(which was unlike him) ya wuni da kayan da ya je asibiti dasu, idanun sa duk sun tasa kamar na
wanda ya yi kuka ko ya kwana ido biyu da nannauyan barci. Ya gaida Daddy da Mama cikin sauri zai wuce, sannan kafin a yi masa kowacce tambaya
Sarham ya kama hanyar fita, sai da ya kai bakin kofa sannan yace musu zai koma asibiti ya
dawo yayi mantuwa ne ba jimawa zai yi ba. Ya kara da cewa kada su damu ba wani abu ne ya
same shi ba, lafiyar sa kalau. Ya dubi Sumayyah yace ki je ki dauke farantin da kika tokaremin
kofa da shi. Daga haka ya fice. Duk suka bishi da ido har ya fice daga main falon, sun kasa
dakatar da shi.
Yana tafe cikin yar karamar motar sa Honda Prelude ta yayin samari yan gata mai kofa
daya, wadda Abba Prof. yayi masa kyautar ta, bayan kammala karatun sa da dawowar sa gida
daga kasa mai tsarki matsayin cikakken likitan ido (at a very young age), yana tafe yana tunanin
makasudin sake fitowar sa daga gida yanzu menene? Tunani kawai ya yi bai kamata ya bar Hauwa da Innar ta su tafi gida ba su ko yi sallama ba,
don haka ya baro su a asibitin dazu (absent-minded) ya tafi gida don ya samu nutsuwar ran sa,
bayan sallamar da asibiti yayi musu a yau (wato discharge). Son samu ma ya tambayi inda
suke, don watan watarana. A fahimtar sa dai, idanun Hauwa ya gama tafiya kuma ta sanadin sa. Wannan tunanin kadai
yana matukar daga hankalin Dr. Sarham kamar ba likita ba, yana kuma azabtar da zuciyar sa,
kasancewar bai taba aikin da bai yi nasara ba sai wannnan karon kan na Hauwa, shi ko kiyashi
baya so ya ji rauni a hannun sa, watakila don wannan ne karo na farko da yayi aikin cataract ya
kuma fara da rashin nasara.
Har ya iso asibitin Murtala yana share zufa daga kan goshin sa da farin hankacin sa, da
zara-zaran yatsunsa.
Ya karya kan motar zai shiga asibitin kenan sai ya hango Innar Hauwa dauke da dan kunshin
kayansu a kan ta, ta kamo hannun Hauwa suna fitowa daga cikin asibitin.
Don haka da hanzari Sarham ya juya kan motar sa zuwa inda ya hange su, yayi gaba da su
kadan ya tsaya, sannan ya fito daga motar ya nufe su.
Inna har kun fito ne? Sarham ya fada da karyayyar muryar data idasa karyewa a wannan
lokacin, idanun sa fal kulawa da damuwa, bayan ya fito daga motar sa, ya maida kofar ya rufe
ya tako a hankali zuwa inda suke a bakin titi suna jiran motar haya.
Da fara Inna ta amsa Mun fito likita, zamu taka zuwa gida, gashi har ka je gida ka dawo bamu
tafi ba muna kailula don tun dazun anka sallame mu.
Kulu ce ta ce in bari ta kara jin karfin jikin ta bazata iya doguwar tafiya a dazun ba.
Idanun Sarham fal damuwa, ya daga ido ya dubi Hauwan, ga idanu tar a bude, manya dasu,
masu haske kamar an wanke su an kuma kara musu lafiya, unfortunately sun koma gululu,
kuma ta sanadin aikin hannun sa, sai jujjuyawa kawai suke a kan titi.
Shin ta yaya zai yi ya daina damuwa a kan aikin nan da yayi ba nasara? Naturally shi mutum
ne mai phobia na gudun zuciyar mutanen da yasan ya batawa, yawan tausayi ga marassa lafiya
da masu karamin karfi, balle ga mata da kuma kananan yara. Shiyasa kannen sa mata biyu ke
tsananin jin dadin sa da kaunar sa, saboda kulawar sa garesu.
Sai ya saka hannu ya karbi kullin kayan su da ke kan Innar Hauwa, ya ce ku yi min alfarma
Inna in raka ku zuwa gida, ko don in ga wuri. Ni dan ki ne, wace unguwa kuke?
Inna ta ce cikin mamaki anya dan nan ma saka ka wahala haka? Can muke da dan nisa, a
can bayan Badalar kofar Naisa. Tuni kafin ta gama fada Sarham ya isa ga motarsa ya saka
kayan nasu a bayan motar, ya budewa Inna da Hauwa kofar gidan baya.
Babu komai Inna, don Allah ku shigo in kai ku. Inna bata da zabi ban da kama hannun
Hauwa ta shigar da ita bayan motar, don ta kasa tankwabe tasirin da kirkin sa da kamalar sa da
jin kan sa yayi a ranta.
Dr. Sarham ya shigo ya tada motar ya juya ta suka fita daga asibitin Murtala gabadaya.
Ba jimawa suka hau titin da zai sada su da Kofar Naisa. Suna tafe a hanya Inna na nuna masa
inda zai bi da su, lokacin da suka shiga cikin Ganuwa.
Hauwa dai bata cewa ko uffan, abinda ya dameta ya dameta, tana dai jin su jefe-jefi suna
hira shi da Inna a kan ta. A surutu irinna Inna har tana gaya masa wai Hauwa yar makaranta ce,
tana aji biyu na sakandire a GGSS Shekara, ta yi jarrabawar shiga aji na uku yanzu, suna
zaman jiran fitowar ta (jarrabawar) Hauwa ta fara apolo. Can kuma ta nisa tace, umh! Yanzu kuwa Hauwa-Kulu ai sai zaman gida ko? Tunda dai
idanu sun tafi?.
Ta yi maganar cikin wata irin murya kamar mai neman amsa daga gare shi, a lokacin da
bawa ya rasa abinda ya kamata yayi akan wata babbar masala data tunkaro shi ba shiri. Dr.
Sarham yayi shiru, yana cigaba da tukin mota, bai ce komai ba don duk wani blame na
makancewar Hauwa ya rasa me yasa ya daukeshi bakidaya ya dora shi a kan sa, bayan kuma
ba haka aikin likita ya gada ba.
A kaidar aikin sa bashi da laifi. Amma a humanity da dattaku irin nasa ji yake shine sila, shine
cause kuma shine at fault.
Daidai lokacin suka iso lokon gidan su Hauwa. Daga inda mota bazata iya shiga ba,
Inna ta nuna masa inda zai iya aje motar ta ce sun gode zasu karasa da kan su a kafa daga
nan, don gidan na su can cikin loko ne mota bata kaiwa.
“Inna ai har gida zan kai ku, bani kayan in rike miki, zan so ganin gidan naku don
watarana in dinga gaishe ki, ina ganin lafiyar idon kanwata. Inna ta ce to likita muna godiya
kwarai, kamar ka san bata da dan uwa. Allah ya yi albarka ya baka masu yi maka kai ma.
Daga haka Inna ta wuce gaba Dr. Sarham ya bi bayan ta zuwa cikin lokon su tana rike
da Hannun Hauwau yana dauke da kunshin kayan su.
Sarham yayi ta mamakin sanayyar jamaar unguwar da Innar Hauwa yadda duk inda
suka bulla jamaar unguwar ke gaida Innar Hauwa cikin girmamawa suna kuma tambayar ta
yaya Hauwa da ido?
Inna sai ta ce sauki na wajen Allah tunda yanzu Hauwa ido babu! Kamar yaya ido babu?
Anan kam saidai tayi murmushi ta sa kai ta wuce su tana mai cewa “da sauki dai”. Ta kasa
bayani don kada ta karasa Sarham a blame. Sosai kowa ya kasa ganewa haka dai ake ta
jajantawa ana wucewa har suka shiga gidan su. Dabbobin Inna duk sun bata gidan da kashin su da fitsarin su yayi daka-daka,
kasancewar ta kwana biyu bata nan ba wanda ke sharewa, duk sun cakalkala gidan, ga
ganyayyaki sun zubo a kaina irin busassun ganyen bishiyoyin su na darbejiya da umbrella duk
gidan ya yi kaca-kaca.
Inna ta shiga dakin ta ta dauko ma Sarham kujera yar tsugunno tana cewa cikin takaicin
yadda ya tadda gidan nasu daka-daka,
kayi hakuri Likita, gidan namu yayi datti, tumaki sun bata shi kwana biyu da bama nan, sun yi
abunda suka ga dama a tsakar gidan nan. Ka ga nan shine gidan namu, ana cewa gidan gidan
Malam Bilyaminu Kofar Naisa”, ko da nan gaba ka zo ka bata ko ka kasa ganewa, haka zaka
ce, ko gidan su Hauwa-Kulu. Sarham yayi murmushi yana jinjina surutu irin na Inna, duk surutun sa ya samu Inna ta fi
shi iyawa, don haka da alama tasu zata zo daya kamar Kakar sa Haj. Kulu yake jin
maganganun nata, ya zauna a kujerar da Inna ta aje masa yana walainiya da kayatattun idanun
sa a gidan, sosai yake shaawar rayuwa irin ta cikin Badala irin wannan, don suma da can a
bayan Badalar suke ta kofar Gadon kaya, amma tun sanda aka bude sabuwar Jamiar Bayero
aka maida mahaifin sa gidajen malamai na ‘New Site’, kasancewar a lokacin yana daya daga
daidakun tsafaffin malamai masu matsayin Farfesa a tsangayar magani (medicine).
A can baya kafin a gina ‘New Site’ din iyayensa suna zauna ne a unguwar Kofar Gadon
Kaya.
Suka sake sosai a tsakar gida suna cafkar hira shi da Inna, (they are all talkatives)
kamar wasu yara. Hauwa na daga can cikin dakinta a kwance, kan siririyar katifar audugar ta,
tana jin su da rabin hankalin ta, amma rabi baya tare da su sam. Ita kadai ta san me take (going
through) wato me take fama da shi a zuciyar ta, wadda ke cike taf da rauni da karaya da
rayuwa, idan ta shafa idanun ta taga duhu didim! Idan ta kyafta su taga babu komai a gabanta
sai duhu! Shin wai shikenan haka zata dauwama har abada cikin duhun idanuwa bazata kara
ganin